Home Labarai Hatsarin jirgin ƙasa ya kashe aƙalla mutum uku a Legas

Hatsarin jirgin ƙasa ya kashe aƙalla mutum uku a Legas

An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum uku, yayin da wasu da dama suka samu rauni lokacin da jirgin ƙasa ya buge wata motar bas da safiyar Alhamis a yankin Ikeja da ke jihar Legas.

Shugaban Hukumar agajin gaggauwa ta ƙasa (NEMA), na yankin kudu maso yammacin Najeriya, Ibrahim Farinloye shi ne ya tabbatar da lamarin.

A baya jami’in ya ce mutum biyu ne, sai dai daga bisani ya ce yawan waɗanda suka mutu ɗin ya ƙaru zuwa uku.

Ya ce “mata biyu ma’aikatan gwamnatin jiha da wani namiji ne suka rasu.”

Motar bas ɗin wadda ta gwamnatin jiha ce na ƙoƙarin tsallaka hanyar jirgin ƙasa ta PWD/Sogunle ne a lokacin da jirgin, wanda ya fito daga Abeokuta zuwa cikin birnin Legas ya yi awon-gaba da ita.

Mai magana da yawun Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas, Adebayo Taofiq shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ana dai ci gaba da aikin ceto, domin tabbatar da cewa babu sauran wanda abin ya rutsa da shi a maƙale.

Mutane sun rinƙa yaɗa hotunan da suka fito daga wurin da haɗarin ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp