Home DUNIYA Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Wata kungiyar kare hakkin dan adam a Burkina Faso ta ce adadin fararen hula da aka kashe a kauyen Karma da ke yankin arewacin Burkina Faso a ranar 20 ga watan afrilun nan, ya kai 136, cikinsu akwai mata 50 da kananan yara 21.

Kididdigar da kungiyar ta fitar a ranar juma’a da ta gabata game da kisan ya kuma nuna jarirai 30, ‘yan kasa da wata 1 na daga cikin wadanda mayakan suka kashe.

Wasu ‘yan bindiga sanye da kayan soji ne suka farwa kauyen, inda  suka yi wa mutane da dama kisan gilla, harin da ke zuwa bayan wanda wasu mayaka masu ikirarin jihadi suka kai wani wuri kusan da kauyen Karma a ranar 15 ga watan Afrilun nan inda suka kashe sojoji 6 da wsu 34.

Kungiyar ta kuma ce baya ga wadannan, maharan sun kuma farwa wasu kauyuka na daban, inda suka kashe mutane 6 a kauyen Dinguiri, wasu 2 a Ménè, sannan suka kashe wasu mutanen 3 a kan hanyar dake tsakanin kauyukan Ouahigouya da Barga.

Adadin mamatan da alkalin Ouahigouya dake yankin arewacin kasar ya sanar a ranar lahadi na nuna kusan mutane 60 aka kashe a mabanbantan hare haren, saidai mazauna kauyen Karma da wasu shaidun gani da ido sun ce adadin ya zarce 100.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp