Home DUNIYA Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Wata kungiyar kare hakkin dan adam a Burkina Faso ta ce adadin fararen hula da aka kashe a kauyen Karma da ke yankin arewacin Burkina Faso a ranar 20 ga watan afrilun nan, ya kai 136, cikinsu akwai mata 50 da kananan yara 21.

Kididdigar da kungiyar ta fitar a ranar juma’a da ta gabata game da kisan ya kuma nuna jarirai 30, ‘yan kasa da wata 1 na daga cikin wadanda mayakan suka kashe.

Wasu ‘yan bindiga sanye da kayan soji ne suka farwa kauyen, inda  suka yi wa mutane da dama kisan gilla, harin da ke zuwa bayan wanda wasu mayaka masu ikirarin jihadi suka kai wani wuri kusan da kauyen Karma a ranar 15 ga watan Afrilun nan inda suka kashe sojoji 6 da wsu 34.

Kungiyar ta kuma ce baya ga wadannan, maharan sun kuma farwa wasu kauyuka na daban, inda suka kashe mutane 6 a kauyen Dinguiri, wasu 2 a Ménè, sannan suka kashe wasu mutanen 3 a kan hanyar dake tsakanin kauyukan Ouahigouya da Barga.

Adadin mamatan da alkalin Ouahigouya dake yankin arewacin kasar ya sanar a ranar lahadi na nuna kusan mutane 60 aka kashe a mabanbantan hare haren, saidai mazauna kauyen Karma da wasu shaidun gani da ido sun ce adadin ya zarce 100.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp