Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Yan majalisar dattawa da suka Fito daga Yankin arewacin Nijeriya sun kalubalanci yunkurin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, na amfani da karfin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Sun bayyana haka ne a yayin da shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rubuta wasika ga majalisar dattawan kasar yana neman amincewarta don daukar matakin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Shugaban ya kuma nemi izinin daukar wasu matakai ciki har da katse wutar lantarkin da Nijeriya ke bai wa Nijar.

Mai Magana Da Yawun Kungiyar Kuma Sanatan Kano ta kudu Sanata Abdurrahman kawu sumaila yace Baza su amince da duk wani Mataki na yaki da Nijeriya da Jamhuriyar Niger ba, Saboda doguwar alakar Dake tsakanin Yankin arewacin Nigeria da ita.

Shugaban majalisar dattawan kasar Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar da Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisar a zaman da ta yi ranar Juma’a.

Ya aike da wasikar ne bayan rashin nasarar tawagar da kungiyar ECOWAS ta tura Nijar don tattaunawa da sojojin kasar don mayar da Shugaba Mohamed Bazoum kan karagar mulki.

Tuni dai sojojin ECOWAS suka fara nuna bukatar su na afkawa dakarun sojin na Nijar domin dawo da Kasar turbar Damukradiyya.

PRNigeria Nijeriya

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 17 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 59 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com