Home DUNIYA Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Yan majalisar dattawa da suka Fito daga Yankin arewacin Nijeriya sun kalubalanci yunkurin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, na amfani da karfin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Sun bayyana haka ne a yayin da shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rubuta wasika ga majalisar dattawan kasar yana neman amincewarta don daukar matakin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Shugaban ya kuma nemi izinin daukar wasu matakai ciki har da katse wutar lantarkin da Nijeriya ke bai wa Nijar.

Mai Magana Da Yawun Kungiyar Kuma Sanatan Kano ta kudu Sanata Abdurrahman kawu sumaila yace Baza su amince da duk wani Mataki na yaki da Nijeriya da Jamhuriyar Niger ba, Saboda doguwar alakar Dake tsakanin Yankin arewacin Nigeria da ita.

Shugaban majalisar dattawan kasar Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar da Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisar a zaman da ta yi ranar Juma’a.

Ya aike da wasikar ne bayan rashin nasarar tawagar da kungiyar ECOWAS ta tura Nijar don tattaunawa da sojojin kasar don mayar da Shugaba Mohamed Bazoum kan karagar mulki.

Tuni dai sojojin ECOWAS suka fara nuna bukatar su na afkawa dakarun sojin na Nijar domin dawo da Kasar turbar Damukradiyya.

PRNigeria Nijeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp