Home DUNIYA Ana shirin kawo karshen yakin gaza ta hanyar diplomasiyyar

Ana shirin kawo karshen yakin gaza ta hanyar diplomasiyyar

An sake dawo da ƙoƙarin bin hanyar diflomasiya domin kawo ƙarshen yaƙin Gaza, inda ake sa rai wakilai daga Hamas za su ci gaba da tattaunawa a birnin Alƙahira na Masar.

An rawaito wani babban kwamandan Hamas na cewa basu da matsala da sabon daftarin yarjejeniyar da Isra’ila ta gabatar kan tsagaita wuta da sakin fursunoni.

Sai dai babu alamar da ke nuna za a cimma daidaituwar.

Rahotanni na cewa sabbin bayanan yarjejeniyar sun ƙunshi dawo da kwanciyar hankali a Gaza, wanda tabbas za su dadaɗa wa Hamas.

Mataimakin kakakin majalisar Isra’ila Moshe Tur- Paz, ya nuna cewa abin da ya kamata a fi bai wa fifiko a yanzu shi ne dawo da mutanensu da ke garƙame gida.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya je Saudiyya, inda shi ma yake tattaunawa da shugabannin Larabawa kan yiwuwar cimma yarjejeniya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp