Home DUNIYA Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta...

Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta cikinta

Kasar Benin ta dauki matakin hana fitar da man da ake fitarwa daga Nijar ta hanyar bututun mai da ya hada rijiyoyin mai na Nijar ta tashar ruwan Cotonou.

Wannan matakin martani ne kai tsaye ga Nijar, wadda ke ci gaba da rufe kan iyakarta da Benin, duk da cewa Ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ɗage takunkumin da ta kakaba wa gwamnatin Nijar.

Sakamakon haka, ayyukan jiragen ruwa da aka keɓe don jigilar mai a halin yanzu ya tsaya cak.

An sanar da jakadan kasar China da ke kasar Benin, Peng Jingtao, tare da hukumar kula da bututun mai, Wapco, a hukumance kan wannan takunkumin.

Ana gudanar da hada-hadar da ta kai na kuɗi sama da CFA biliyan 600 ta hanyar bututun man na Nijar wanda ya ratsa ta cikin ƙasar Benin.

Gamayyar kamfanonin kasar Sin ne suka samar da bututun man mai tsawon kilomita 2,000 da kuma rijiyoyin mai na kasar Nijar.

An kammala aikin bututun man fetur ɗin wanda ake sa ran zai rika jigilar ganga 90,000 na mai a kowace rana zuwa tashar fitar da kaya a kasar Benin a farkon wannan shekarar.

Sai dai kuma rashin jituwar da ke tsakanin ƙasashen biyu bayan juyin mulkin watan Yulin 2023 da ya hambarar da shugaba Mohamed Bazoum na iya kawo cikas ga aikin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp