Home General Kwankwaso ya zargi Bola Tinubu da dagula komai a Nijeriya

Kwankwaso ya zargi Bola Tinubu da dagula komai a Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP a kasar nan, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kira ga ‘yan ƙasar da ke shirin gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa da su yi amfani da ƙuri’arsu wajen sauya shugabannin, maimaikon fitowa zanga-zangar.

Kwankwaso ya ce ƙasar ta tsinci kanta a halin matsin rayuwa da take ciki ne sakamakon kasa ɗaukar matakan da suka dace da jagororin ƙasar suka yi tun a shekarar 2007.

Cikin wata sanarwa da jagoran Kwankwansiyyar ya fitar ya ce har yanzu lokaci bai ƙure ba, na yadda za a farfaɗo da ƙasar da samar wa al’umma abubuwan ci-gaba da na walwala.

Ya ci gaba da cewa hakan zai yiwu ne kawai ta hanyar samar da shugabanci nagari, da bin doka da kyakkyawan tsari dayin abubuwa yadda suka dace.

Inda yace abin takaici ne yadda halayen shugabanninmu na rashin iya mulki suka jefa ƙasar nan musamman matasa cikin yunwa da rashin tsaro da fusata ta yadda har wasu daga cikinsu suka fara yanke ƙauna game da gyaruwar ƙasar,

Wasu matasan Najeriyar na shirin gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna damuwarsu kan halin matsi da tsadar rayuwa da sauran matsalolin da al’ummar ƙasar ke fuskanta.

To sai dai Kwankwaso ya zargi gwamnatin tarayya da hannu a haifar da wasu matsalolin da ƙasar ke fuskanta.

”Sa bakin gwamnatin tarayya a batun sarautar Kano, da tsige mataimakin gwamnan Edo da rikicin siyasar jihar Rivers da yi wa matatar mai ta Dangote zagon-ƙasa, da ce-ce-ce-ku-cen da yarjejeniyar SAMOA ta haifar, da rikici tsakanin Sanata Ali Ndume da APC, da rashin tsaro da sauran miyagun laifukan da za a iya kauce musu na daga cikin misalan abubuwan da suka haifar da matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan”, in ji Kwankwaso.

Jagoran NNPP ya ce duk da cewa zanga-zangar adawa da tsadar rayuwar, hanya ce da matasan za su nuna wa shugabbanni damuwarsu, amma ya ce yana da kyau matasan da ke shirin gudanar da zanga-zangar su sanya muradun ƙasar a gaba fiye da komai.

Ya kira ga matasan ƙasar su zama masu haƙuri da gwamnatin, ta hanyar ba ta duk wata dama da goyon baya domin ta cimma nasara.

”A ƙarshe duk shugabannin da suka gaza, muna da dama a matsayinmu na ‘yan ƙasa mu yi amfani da ƙuri’unmu, don zaɓar wasu da muke ganin za su kawo mana ci gaban da muke buƙata”, in ji shi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp