Home Labarai CISLAC ta bukaci Gwamnatin Nijeriya ta magance matsalar yunwa a kasar

CISLAC ta bukaci Gwamnatin Nijeriya ta magance matsalar yunwa a kasar

Kungiyar Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam da Kuma Sanya Idanu akan ayyukan Yan Majalisun Ƙasar nan CISLAC, ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta fito da Tsare Tsare da Zasu Amfani al’ummar Kasa maimakon Kara ta’azzara Zanga Zanga.

Wannan na cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar Auwal Musa Rafsanjani ya Fitar, wadda tace Wajibi ne Gwamnati Ta Dauki Matakin Gaggawa a bangarorin, Yunwa – Rashin aikin yi- Matsalar Tsaro – hau- hawar Farashin kayayyaki – Cin hanci da rashawa Wanda Sune Suka zubar da kimar Hukumomin Gwamnati

Ya Kara da Cewa Daukar matakin gaggawa a Wadannan bangarorin shine Zai baiwa Yan Nigeria kwarin Gwiwar Jin Cewa shugabanin Ƙasar sun damu da halin da suke Ciki.

kwamarade Auwal Musa Rafsanjani yace Wajibi ne Gwamnatin Tarayya da jami’an tsaro su baiwa al’umma kariya Yayin Gudanar da Zanga Zangar Lumana Kamar Yadda Tsarin Mulki ya Tanadar

Kwamarade Rafsanjani ya Kuma Gargadi Jami’an Tsaro na soji da Cewa su Kaucewa Shiga duk Wani hurumin da ba nasu ba, Inda Yace Yan Sanda da Kuma Jami’an Tsaro na Farin Kaya DSS Sune da Alhakin Sanya Idanu akan Yadda Zanga Zangar Lumana Zata Kasance

akashe ya Bukaci Masu Zanga Zangar da su Tabbatar Cewa Wasu Batagari basuyi Amfani dasu Wajen Tayar da tarzoma ba, Dan haka Yace Wajibi Masu Zanga Zangar su Sanya Idanu Sosai

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp