Home Labarai Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojin haɗin gwiwarta ta Operation haɗin kai da JTF a Arewa maso Gabashin ƙasar sun samu nasarori a gagarumin samamen da suka gudanar da ake kira da Operation DESERT SANITY, inda suka lalata sansanonin ‘yanbindiga da dama tare da ƙwace makamai da kayan yaƙi.

Sojojin sun kuma daƙile hare-haren da aka shirya a yankin Timbuktu Triangle a lokacin samamen.

Sanarwar da rundunar ta fitar wa manema labarai ta ce a ranar Lahadi, 18 ga Janairu, 2026, sojoji sun tashi daga wuraren da suke tsarewa inda suka gudanar da samamen bisa bayanan sirri a kan wasu sansanonin ‘yanbindiga da aka gano, ciki har da Chilaria, Garin Faruk da Abirma.

A yayin samamen, an samu kwatar kayan soji da dama, ciki har da wayoyi, rediyo, harsasai, bindigogi na AK-47 guda 5, tutocin Boko Haram/ISWAP, kayan aikin noma, motar daukar kaya, da man fetur, da sauran kayayyakin yaƙi na ‘yanbindiga.

Sojojin sun fuskanci harin jiragen sama marasa matuki daga ‘yanbindiga a lokacin samamen, amma hakan bai hana su ci gaba da gudanar da ayyukansu ba.

Haka kuma, an dakile wani harin a yammacin ranar, wanda ya tilasta wa ‘yanbindiga ja da baya, abin da ya nuna cikakken rinjayar sojoji a yankin da kuma ƙarfin su wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp