Home Labarai Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojin haɗin gwiwarta ta Operation haɗin kai da JTF a Arewa maso Gabashin ƙasar sun samu nasarori a gagarumin samamen da suka gudanar da ake kira da Operation DESERT SANITY, inda suka lalata sansanonin ‘yanbindiga da dama tare da ƙwace makamai da kayan yaƙi.

Sojojin sun kuma daƙile hare-haren da aka shirya a yankin Timbuktu Triangle a lokacin samamen.

Sanarwar da rundunar ta fitar wa manema labarai ta ce a ranar Lahadi, 18 ga Janairu, 2026, sojoji sun tashi daga wuraren da suke tsarewa inda suka gudanar da samamen bisa bayanan sirri a kan wasu sansanonin ‘yanbindiga da aka gano, ciki har da Chilaria, Garin Faruk da Abirma.

A yayin samamen, an samu kwatar kayan soji da dama, ciki har da wayoyi, rediyo, harsasai, bindigogi na AK-47 guda 5, tutocin Boko Haram/ISWAP, kayan aikin noma, motar daukar kaya, da man fetur, da sauran kayayyakin yaƙi na ‘yanbindiga.

Sojojin sun fuskanci harin jiragen sama marasa matuki daga ‘yanbindiga a lokacin samamen, amma hakan bai hana su ci gaba da gudanar da ayyukansu ba.

Haka kuma, an dakile wani harin a yammacin ranar, wanda ya tilasta wa ‘yanbindiga ja da baya, abin da ya nuna cikakken rinjayar sojoji a yankin da kuma ƙarfin su wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp