Home Labarai JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Haɗakar ƙungiyoyin ma’aikatan lafiya ta Najeriya, (JOHESU) ta ce ‘yan Najeriya su ɗora wa gwamnatin tarayya alhakin wahalhalun da marasa lafiya da sauran masu buƙatar kulawar lafiya ke fuskanta sakamakon yajin aikin da mambobinta ke yi.

Ƙungiyar ta ce buƙatarta ɗaya tilo ita ce aiwatar da rahoton da ya shafi daidaita tsarin albashin ma’aikatan kiwon lafiya na CONHESS.

Sakataren JOHESU na ƙasar, Martin Egbanubi ne ya bayyana hakan ne a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

Ya ce duk da sanin tasirin yajin aikin a kan ƴanƙasa, bai kamata a ɗora musu laifi ba.

Ya ce, “Mun san irin tasirin da yajin aikin ke yi wa ‘yan Najeriya, amma bai kamata ‘yan ƙasa su ɗora mana laifi ba. Gwamnati ce ya kamata ta ɗauki alhaki, domin ita ce ke da haƙƙin yin abin da ya dace domin kauce wa irin wannan yajin aiki a nan gaba.”

Egbanubi ya ƙara da cewa JOHESU na fahimtar halin da marasa ƙarfi ke ciki, musamman waɗanda ba su da ƙarfin zuwa asibitoci masu zaman kansu, amma ya ce mambobin ƙungiyar ma suna shan wahala.

Saboda haka, ƙungiyar ta buƙaci masu kishin kasa su yi kira ga gwamnati ta gaggauta magance buƙatar domin dakatar da yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp