Home Labarai JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Haɗakar ƙungiyoyin ma’aikatan lafiya ta Najeriya, (JOHESU) ta ce ‘yan Najeriya su ɗora wa gwamnatin tarayya alhakin wahalhalun da marasa lafiya da sauran masu buƙatar kulawar lafiya ke fuskanta sakamakon yajin aikin da mambobinta ke yi.

Ƙungiyar ta ce buƙatarta ɗaya tilo ita ce aiwatar da rahoton da ya shafi daidaita tsarin albashin ma’aikatan kiwon lafiya na CONHESS.

Sakataren JOHESU na ƙasar, Martin Egbanubi ne ya bayyana hakan ne a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

Ya ce duk da sanin tasirin yajin aikin a kan ƴanƙasa, bai kamata a ɗora musu laifi ba.

Ya ce, “Mun san irin tasirin da yajin aikin ke yi wa ‘yan Najeriya, amma bai kamata ‘yan ƙasa su ɗora mana laifi ba. Gwamnati ce ya kamata ta ɗauki alhaki, domin ita ce ke da haƙƙin yin abin da ya dace domin kauce wa irin wannan yajin aiki a nan gaba.”

Egbanubi ya ƙara da cewa JOHESU na fahimtar halin da marasa ƙarfi ke ciki, musamman waɗanda ba su da ƙarfin zuwa asibitoci masu zaman kansu, amma ya ce mambobin ƙungiyar ma suna shan wahala.

Saboda haka, ƙungiyar ta buƙaci masu kishin kasa su yi kira ga gwamnati ta gaggauta magance buƙatar domin dakatar da yajin aikin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp