Home Taska Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

Protest Insecurity

Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

 

A ranar Asabar, masu zanga-zanga sun tare gadar da ke kan hanyar Karu zuwa Nyanya, wacce ta haɗa Abuja da Jihar Nasarawa.

Masu zanga-zangar na neman a inganta tsaro saboda yawaitar sace-sacen mutane da hare-hare.

Sun riƙe kwalaye masu rubutu tare da rera waƙoƙi suna zanga-zanga, suna cewa gwamnati dole ta ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyi.

Sun taru a kan gadar yankin, sannan daga baya suka yi tattaki zuwa Nyanya.

Wannan ya jawo cunkoson ababen hawa a kan hanyar Abuja zuwa Keffi, inda matafiya da dama suka maƙale na tsawon sa’o’i.

Masu zanga-zangar sun ce rayuwa ta yi wahala saboda rashin tsaro, kuma sun buƙaci gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa.

An tura jami’an tsaro domin sanya ido da kuma kula da zirga-zirgar ababen hawa.

An kuma shawarci direbobi su bi wasu hanyoyi daban.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu rahoton tashin hankali ko raunuka ba, amma an tare hanyar lamarin da kawo tsaiko ga masu ababen hawa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa
X whatsapp