Home Labarai Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin kasa (COAS) Laftanar Janar Faruk Yahaya, ya taya Sojojin Nijeriya murnar bikin Sallah Kara.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke sa hannun daraktan yada labaran Rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, takardar dake da kwanan watan 29 ga watan Afrilun 2022, ta mabaci laftanar Janar Yahaya na kalaman yayin da yake mika sakon fatan alheri ga ma’aikatan rundunar sojin kasar nan a duk inda suke a fadin Nijeriyar da kuma yabawa bisa ga sadaukarwasu da jajircewar da suke nunawa akan ayyukan su na kare martabar Nijeriya.

Babban hafsan sojin a bukaci dakarun rundundar da su kara kaimi wajen cigaba da gudanar ayyukan alkhairin da suka gudanar a watan ramadan, tare kuda mayar da hankali wajen sauke nauyi da ya rataya a wuyan su kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada.

Ya bukaci kwamandojin yakin da su rubunya kokarin si a cigaba da gudanar da ayyukan su, daga bisani ya bayyana cewa goron sallar da yake bukata dagagare su shine su tabbatar da sun kawar da ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane tare da kwato makamai daga hannun su.

Janar Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin addu’a ga sojojin da suka rasa rayukan su wajen kare martaba da muhibbar Nijeriya.

Ya kuma kara cewar a karkashin shugabancin sa  jami’an zasu cigaba da samun horo tare da lura da iyalan su, inda ya bada tabbacin cigaban da baiwa wadanda sula sami rauni a yayin gudanar da aikin kare wannan kasa, tare da basu kulawa ta musamman da zata taimawa musu wajen dawo da lafiyar su kamar yadda suke a da.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp