Home Labarai Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin kasa (COAS) Laftanar Janar Faruk Yahaya, ya taya Sojojin Nijeriya murnar bikin Sallah Kara.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke sa hannun daraktan yada labaran Rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, takardar dake da kwanan watan 29 ga watan Afrilun 2022, ta mabaci laftanar Janar Yahaya na kalaman yayin da yake mika sakon fatan alheri ga ma’aikatan rundunar sojin kasar nan a duk inda suke a fadin Nijeriyar da kuma yabawa bisa ga sadaukarwasu da jajircewar da suke nunawa akan ayyukan su na kare martabar Nijeriya.

Babban hafsan sojin a bukaci dakarun rundundar da su kara kaimi wajen cigaba da gudanar ayyukan alkhairin da suka gudanar a watan ramadan, tare kuda mayar da hankali wajen sauke nauyi da ya rataya a wuyan su kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada.

Ya bukaci kwamandojin yakin da su rubunya kokarin si a cigaba da gudanar da ayyukan su, daga bisani ya bayyana cewa goron sallar da yake bukata dagagare su shine su tabbatar da sun kawar da ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane tare da kwato makamai daga hannun su.

Janar Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin addu’a ga sojojin da suka rasa rayukan su wajen kare martaba da muhibbar Nijeriya.

Ya kuma kara cewar a karkashin shugabancin sa  jami’an zasu cigaba da samun horo tare da lura da iyalan su, inda ya bada tabbacin cigaban da baiwa wadanda sula sami rauni a yayin gudanar da aikin kare wannan kasa, tare da basu kulawa ta musamman da zata taimawa musu wajen dawo da lafiyar su kamar yadda suke a da.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp