Home Labarai Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin Nijeriya , Ya Taya Sojojin Kasar Murnar Bikin Sallah.

Babban Hafsan Sojin kasa (COAS) Laftanar Janar Faruk Yahaya, ya taya Sojojin Nijeriya murnar bikin Sallah Kara.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke sa hannun daraktan yada labaran Rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, takardar dake da kwanan watan 29 ga watan Afrilun 2022, ta mabaci laftanar Janar Yahaya na kalaman yayin da yake mika sakon fatan alheri ga ma’aikatan rundunar sojin kasar nan a duk inda suke a fadin Nijeriyar da kuma yabawa bisa ga sadaukarwasu da jajircewar da suke nunawa akan ayyukan su na kare martabar Nijeriya.

Babban hafsan sojin a bukaci dakarun rundundar da su kara kaimi wajen cigaba da gudanar ayyukan alkhairin da suka gudanar a watan ramadan, tare kuda mayar da hankali wajen sauke nauyi da ya rataya a wuyan su kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada.

Ya bukaci kwamandojin yakin da su rubunya kokarin si a cigaba da gudanar da ayyukan su, daga bisani ya bayyana cewa goron sallar da yake bukata dagagare su shine su tabbatar da sun kawar da ‘yan ta’adda masu garkuwa da mutane tare da kwato makamai daga hannun su.

Janar Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin addu’a ga sojojin da suka rasa rayukan su wajen kare martaba da muhibbar Nijeriya.

Ya kuma kara cewar a karkashin shugabancin sa  jami’an zasu cigaba da samun horo tare da lura da iyalan su, inda ya bada tabbacin cigaban da baiwa wadanda sula sami rauni a yayin gudanar da aikin kare wannan kasa, tare da basu kulawa ta musamman da zata taimawa musu wajen dawo da lafiyar su kamar yadda suke a da.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp