Home Labarai ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a...

ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a kasar Switzerland

Kungiyar Sadarwa ta Kasa da Kasa wato International Telecommunication Union (ITU) ta nada Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, a matsayin shugaban taron kolin kingiyar da gudana a shalkwatar kungiyar dake Geneva a kasar Switzerland.

Kungiyar Ta ITU ta tabbatar da nadin na Pantami ta cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban sakatern ta, wanda ya bayyana cewa kungiyar ta nada Farfesa Pantami matsayin shugaban taron kolin ta.

”Bisa la’akari da sadaukarwarsa ga kungiya, da kuma rawar da yake takawa a cikin tsare tsaren gudanar da taron na WSIS” masu ruwa da tsaki sunga dacewar nadashi bisa wannan matsayi, taron zai sami halartar manyan ministoci daga kasashen dake cikin wannan kungiya.

Dandalin taron na WSIS 2022 na matsayin babban dandalin tattaunawa gami da rawar da hanyoyin sadarwa ke takawa, kuma tana matsayin hanyar aiwatar da manufofin cigaba mai dorewa, bisa la’akari da tsarin da duniya ke kai gami da bibiyar hanyoyin aiwatar da kudirin cigaba mai dorewa zuwa shekarar 2030 na (UNGA Resolution A/&70/1).

Haka zalika dandamalin na WSIS na bin diddigin nasarorin da ake samu bisa hadin Gwiwar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da abin ya shafa, ta hanayar samar da bayanan binciken da suka gudanar.

Taron na WSIS, na kungiyar ITU da asusun tallafawa kananan yar ana majalisar dinkin duniyar da UNCTAD suka shirya tare da hadin wasu hukumomin majalisar dinkin duniyar guda 24, da suka hadar da FAO, ILO, ITC, UNDESA, UNICO, UNITAR, UNHCR, UNODC, UNEP, UPU, UN TECH BANK, WMO, WIPO, WHO, WFP da dai sauransu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp