Home Labarai ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a...

ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a kasar Switzerland

Kungiyar Sadarwa ta Kasa da Kasa wato International Telecommunication Union (ITU) ta nada Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, a matsayin shugaban taron kolin kingiyar da gudana a shalkwatar kungiyar dake Geneva a kasar Switzerland.

Kungiyar Ta ITU ta tabbatar da nadin na Pantami ta cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban sakatern ta, wanda ya bayyana cewa kungiyar ta nada Farfesa Pantami matsayin shugaban taron kolin ta.

”Bisa la’akari da sadaukarwarsa ga kungiya, da kuma rawar da yake takawa a cikin tsare tsaren gudanar da taron na WSIS” masu ruwa da tsaki sunga dacewar nadashi bisa wannan matsayi, taron zai sami halartar manyan ministoci daga kasashen dake cikin wannan kungiya.

Dandalin taron na WSIS 2022 na matsayin babban dandalin tattaunawa gami da rawar da hanyoyin sadarwa ke takawa, kuma tana matsayin hanyar aiwatar da manufofin cigaba mai dorewa, bisa la’akari da tsarin da duniya ke kai gami da bibiyar hanyoyin aiwatar da kudirin cigaba mai dorewa zuwa shekarar 2030 na (UNGA Resolution A/&70/1).

Haka zalika dandamalin na WSIS na bin diddigin nasarorin da ake samu bisa hadin Gwiwar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da abin ya shafa, ta hanayar samar da bayanan binciken da suka gudanar.

Taron na WSIS, na kungiyar ITU da asusun tallafawa kananan yar ana majalisar dinkin duniyar da UNCTAD suka shirya tare da hadin wasu hukumomin majalisar dinkin duniyar guda 24, da suka hadar da FAO, ILO, ITC, UNDESA, UNICO, UNITAR, UNHCR, UNODC, UNEP, UPU, UN TECH BANK, WMO, WIPO, WHO, WFP da dai sauransu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp