Home Labarai Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda...

Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda HDQ

Dakarun tsaro a Nijeriya da suka hada da ‘Yan sanda da sauran jami’an tsaro na cigaba da samun nasara kan tabbatar da ingantaccen tsaro a yankuna 6 na Nijeriya.

Wannan na cikin wata takardar jawabin tsaro darakta yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Benard Onyeuko ya sanyawa hannu mai dauke da kwanan watan 2 ga watan Yunin 2022, wadda taya tana kunshe da jawabin tsaron tun daga 19 ga watan mayu zuwa 2 ga yunin shekarar.

Takardar sanarwar tace dakarun Operation Hadin kai a ranar 22 ga wata mayun wannan shekara tare da hadin gwuiwar Civilian task force sun fatattaki ‘yan ta’adda a maboyar su dake garuruwan Amdaga, balazola, Ndakaine, jango, Sabah da Gobara duk a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno, inda yan ta’addar suk aranta a na kare tare da barin kayayyakin su.

Har ila yau, a ranar 23 ga watan Mayu, 2022, sojoji sun gudanar da sintiri a kan titin tsohowar Marte dake karamar hukuma marte a jihar borno inda suk sami nasara kwato wata mota mallakin hukumar lura da tituna ta jihar da ‘yan ta’adda suka sace a watan fabrerun 2021.

Haka zalika sojojin dake sintiri a yankunan Ashigashiya, kodele, da apagaluwa dake cikin karamar hukumar Gwoza sunyi ta jihar Borno sun yi arangama da ‘yan Ta’addan inda sukayi kazamin artabu har ‘yan ta’addan suka ranat a na kare, yayin da sojojin suka sami nasarar kwato raguna 40.

Cikin wasu makwanni sojojin suka sake gudanar da wani sumame gami da kwanton bauna a yankin Zuyel-Wuno daura da tsaunin shelmi a kauyen Dugushewu, Gwoza, limankare a tsohowar Marte, Sabah, Kancorner, hanyar Gamboru Wulgo, Charaman, hanyar Pulka-Kwadaje, mairammi Tumbun rago, Tumbum Dilla da Jamina, Kawuri Sibiri, Kuwaitu, Kauyen Miya duk a jihar ta Borno.

Daga bisani Oyeuko ya yaba da da kokarin dakarun sojin kasar, tare da tabbatar da sake basu cikakkiyar gudunmawa, tare da godewa daukacin Al’ummar kasar bisa gudunmawar da suke bawa dakarun sojin a kokarin da suke na samar da ingantaccen zaman lafiya mai dorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp