Home Labarai Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda...

Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda HDQ

Dakarun tsaro a Nijeriya da suka hada da ‘Yan sanda da sauran jami’an tsaro na cigaba da samun nasara kan tabbatar da ingantaccen tsaro a yankuna 6 na Nijeriya.

Wannan na cikin wata takardar jawabin tsaro darakta yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Benard Onyeuko ya sanyawa hannu mai dauke da kwanan watan 2 ga watan Yunin 2022, wadda taya tana kunshe da jawabin tsaron tun daga 19 ga watan mayu zuwa 2 ga yunin shekarar.

Takardar sanarwar tace dakarun Operation Hadin kai a ranar 22 ga wata mayun wannan shekara tare da hadin gwuiwar Civilian task force sun fatattaki ‘yan ta’adda a maboyar su dake garuruwan Amdaga, balazola, Ndakaine, jango, Sabah da Gobara duk a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno, inda yan ta’addar suk aranta a na kare tare da barin kayayyakin su.

Har ila yau, a ranar 23 ga watan Mayu, 2022, sojoji sun gudanar da sintiri a kan titin tsohowar Marte dake karamar hukuma marte a jihar borno inda suk sami nasara kwato wata mota mallakin hukumar lura da tituna ta jihar da ‘yan ta’adda suka sace a watan fabrerun 2021.

Haka zalika sojojin dake sintiri a yankunan Ashigashiya, kodele, da apagaluwa dake cikin karamar hukumar Gwoza sunyi ta jihar Borno sun yi arangama da ‘yan Ta’addan inda sukayi kazamin artabu har ‘yan ta’addan suka ranat a na kare, yayin da sojojin suka sami nasarar kwato raguna 40.

Cikin wasu makwanni sojojin suka sake gudanar da wani sumame gami da kwanton bauna a yankin Zuyel-Wuno daura da tsaunin shelmi a kauyen Dugushewu, Gwoza, limankare a tsohowar Marte, Sabah, Kancorner, hanyar Gamboru Wulgo, Charaman, hanyar Pulka-Kwadaje, mairammi Tumbun rago, Tumbum Dilla da Jamina, Kawuri Sibiri, Kuwaitu, Kauyen Miya duk a jihar ta Borno.

Daga bisani Oyeuko ya yaba da da kokarin dakarun sojin kasar, tare da tabbatar da sake basu cikakkiyar gudunmawa, tare da godewa daukacin Al’ummar kasar bisa gudunmawar da suke bawa dakarun sojin a kokarin da suke na samar da ingantaccen zaman lafiya mai dorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp