Home Labarai Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda...

Tsaro: Dakarun Sojin Nijeriya Na Cigaba da Samun Nasara Kan ‘Yan Ta’adda HDQ

Dakarun tsaro a Nijeriya da suka hada da ‘Yan sanda da sauran jami’an tsaro na cigaba da samun nasara kan tabbatar da ingantaccen tsaro a yankuna 6 na Nijeriya.

Wannan na cikin wata takardar jawabin tsaro darakta yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Benard Onyeuko ya sanyawa hannu mai dauke da kwanan watan 2 ga watan Yunin 2022, wadda taya tana kunshe da jawabin tsaron tun daga 19 ga watan mayu zuwa 2 ga yunin shekarar.

Takardar sanarwar tace dakarun Operation Hadin kai a ranar 22 ga wata mayun wannan shekara tare da hadin gwuiwar Civilian task force sun fatattaki ‘yan ta’adda a maboyar su dake garuruwan Amdaga, balazola, Ndakaine, jango, Sabah da Gobara duk a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno, inda yan ta’addar suk aranta a na kare tare da barin kayayyakin su.

Har ila yau, a ranar 23 ga watan Mayu, 2022, sojoji sun gudanar da sintiri a kan titin tsohowar Marte dake karamar hukuma marte a jihar borno inda suk sami nasara kwato wata mota mallakin hukumar lura da tituna ta jihar da ‘yan ta’adda suka sace a watan fabrerun 2021.

Haka zalika sojojin dake sintiri a yankunan Ashigashiya, kodele, da apagaluwa dake cikin karamar hukumar Gwoza sunyi ta jihar Borno sun yi arangama da ‘yan Ta’addan inda sukayi kazamin artabu har ‘yan ta’addan suka ranat a na kare, yayin da sojojin suka sami nasarar kwato raguna 40.

Cikin wasu makwanni sojojin suka sake gudanar da wani sumame gami da kwanton bauna a yankin Zuyel-Wuno daura da tsaunin shelmi a kauyen Dugushewu, Gwoza, limankare a tsohowar Marte, Sabah, Kancorner, hanyar Gamboru Wulgo, Charaman, hanyar Pulka-Kwadaje, mairammi Tumbun rago, Tumbum Dilla da Jamina, Kawuri Sibiri, Kuwaitu, Kauyen Miya duk a jihar ta Borno.

Daga bisani Oyeuko ya yaba da da kokarin dakarun sojin kasar, tare da tabbatar da sake basu cikakkiyar gudunmawa, tare da godewa daukacin Al’ummar kasar bisa gudunmawar da suke bawa dakarun sojin a kokarin da suke na samar da ingantaccen zaman lafiya mai dorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp