Home Labarai Dole Ne Najeriya Ta Kasance Cikin Zaman Lafiya – CDS Irabor Ya...

Dole Ne Najeriya Ta Kasance Cikin Zaman Lafiya – CDS Irabor Ya Fadawa ‘Yan Siyasa

Gabanin Babban zaben shekarar 2023, shalkwatar tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta bukaci ‘yan siyasar kasar da su bi hanyaar data dace wajen cika muradin su.

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya Janar Lucky Irabor ne ya bayyana hakan, yayin da yake wata ganawar mako-mako da manema labarai a birnin tarayyar Abuja.

Yace wajibi ne ‘yan siyasar su bar kasar ta zauna lafiya, ta hanyar gujewa ayyuka da maganganun da ka iya kawo cikas ga tsaron kasar yayin yakin neman zabe.

A cewar Irabor, “Nijeriya kasar mu ce, yanzu hakan mun shiga kakar zabe kuma kowa na bukara a gudanar da zaben da yakin neman zaben cikin lumana, naji dadin yadda shugaban kasa ya shaidawa Al’ummar kasar abinda yake so amma kar a yi tunanin cewa hakkn gwamnati ne ita kai ta tabbatar anyi zaben cikin kwanciyar hankali.

“Abu mafi Muhimmanci dangene da zaben da ke tafe, shi ne mu kasance mazan mu da mata mun ggudanar da shi cikin kwnciyar hankali, kuma ina bukatar ku tura wannan sako zuwa ga kowa da kowa, dukkan wanda yake son yin zabe yayi shi cikin doka da odar, domin kuwa zamu tsaya a gefe muga masu tada tarzoma, domin neman mukamai.

Daga bisani ya bayyana cewa Nijeriya kas ace wacce dole ne a azauna lafiya don haka kada mu bari masu aikata laifi ko ‘yan daba su yi amfani damu wajen wargazata, don haka muna goyon bayan jami’an ‘yan sanda don basu duk wani talafi domin cigaban Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp