Home Labarai Dole Ne Najeriya Ta Kasance Cikin Zaman Lafiya – CDS Irabor Ya...

Dole Ne Najeriya Ta Kasance Cikin Zaman Lafiya – CDS Irabor Ya Fadawa ‘Yan Siyasa

Gabanin Babban zaben shekarar 2023, shalkwatar tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta bukaci ‘yan siyasar kasar da su bi hanyaar data dace wajen cika muradin su.

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya Janar Lucky Irabor ne ya bayyana hakan, yayin da yake wata ganawar mako-mako da manema labarai a birnin tarayyar Abuja.

Yace wajibi ne ‘yan siyasar su bar kasar ta zauna lafiya, ta hanyar gujewa ayyuka da maganganun da ka iya kawo cikas ga tsaron kasar yayin yakin neman zabe.

A cewar Irabor, “Nijeriya kasar mu ce, yanzu hakan mun shiga kakar zabe kuma kowa na bukara a gudanar da zaben da yakin neman zaben cikin lumana, naji dadin yadda shugaban kasa ya shaidawa Al’ummar kasar abinda yake so amma kar a yi tunanin cewa hakkn gwamnati ne ita kai ta tabbatar anyi zaben cikin kwanciyar hankali.

“Abu mafi Muhimmanci dangene da zaben da ke tafe, shi ne mu kasance mazan mu da mata mun ggudanar da shi cikin kwnciyar hankali, kuma ina bukatar ku tura wannan sako zuwa ga kowa da kowa, dukkan wanda yake son yin zabe yayi shi cikin doka da odar, domin kuwa zamu tsaya a gefe muga masu tada tarzoma, domin neman mukamai.

Daga bisani ya bayyana cewa Nijeriya kas ace wacce dole ne a azauna lafiya don haka kada mu bari masu aikata laifi ko ‘yan daba su yi amfani damu wajen wargazata, don haka muna goyon bayan jami’an ‘yan sanda don basu duk wani talafi domin cigaban Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp