Home Labarai ‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

Wasu da ake zargin ‘Yan Ta’adda ne sun yiwa Asibitin Koyar na Jami’ar Jihar Osun dake garin Osogbo tsinke, domin daukar gawar guda cikin abokan ayyukan ta’addanci su da ya mutu sakamako Harbin bindiga.

An ruwaito cewa mutum 2 ne suka mutu sakamakon harin na ‘yan bindigar a ranar talata a garin na Osogbo, sai dai jami’an tsaro na Amotekun sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Daban.

Daga bisani wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun lalata gidan kwamandan Amotekun, Amitolu Shittu, a yayin artabun ne guda cikin su ya sami raunukan Harbin bindiga kuma an kai shi asibitin koyarwa na UNIOSUN domin yi masa magani daga bisani yace mutu.

Majiyar mu ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye asibitin ne da nufin dauko gawar abokin aikinsu amma jami’an kiwon lafiya suka dage kan a basu cikakkun takardu, wanda ‘yan ta’addan suka yi biris da bukatar jami’an asibitin.

Wani shaidar gani da Ido yace, ‘yan ta’addan sun kara karfi inda suka kutsawa cikin harabar Asibitin da muggana makamai da suka hadar da Gatari, Katako, Wukake da dai sauran makamai masu razanarwa, wannan ta sanya jami’an asibitin rufe manyan kofofin asibitin na tsawon sa’oi 2 abinda ya hana su dauke gawar.

Likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aiktan asibitin sun nemi mafaka kafin jami’an tsaro su shiga Tsakani.

Shugaban kwamitin ba da shawara a Asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Osun, Osogbo, Babatunde Afolabi ya tabbatar da faruwar lamarin amma y ace ‘an shawo kan matsalar; bayan sun gudanar da bincike kan gawar an fitar da ita domin binne wa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp