Home Labarai ‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

Wasu da ake zargin ‘Yan Ta’adda ne sun yiwa Asibitin Koyar na Jami’ar Jihar Osun dake garin Osogbo tsinke, domin daukar gawar guda cikin abokan ayyukan ta’addanci su da ya mutu sakamako Harbin bindiga.

An ruwaito cewa mutum 2 ne suka mutu sakamakon harin na ‘yan bindigar a ranar talata a garin na Osogbo, sai dai jami’an tsaro na Amotekun sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Daban.

Daga bisani wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun lalata gidan kwamandan Amotekun, Amitolu Shittu, a yayin artabun ne guda cikin su ya sami raunukan Harbin bindiga kuma an kai shi asibitin koyarwa na UNIOSUN domin yi masa magani daga bisani yace mutu.

Majiyar mu ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye asibitin ne da nufin dauko gawar abokin aikinsu amma jami’an kiwon lafiya suka dage kan a basu cikakkun takardu, wanda ‘yan ta’addan suka yi biris da bukatar jami’an asibitin.

Wani shaidar gani da Ido yace, ‘yan ta’addan sun kara karfi inda suka kutsawa cikin harabar Asibitin da muggana makamai da suka hadar da Gatari, Katako, Wukake da dai sauran makamai masu razanarwa, wannan ta sanya jami’an asibitin rufe manyan kofofin asibitin na tsawon sa’oi 2 abinda ya hana su dauke gawar.

Likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aiktan asibitin sun nemi mafaka kafin jami’an tsaro su shiga Tsakani.

Shugaban kwamitin ba da shawara a Asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Osun, Osogbo, Babatunde Afolabi ya tabbatar da faruwar lamarin amma y ace ‘an shawo kan matsalar; bayan sun gudanar da bincike kan gawar an fitar da ita domin binne wa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp