Home Labarai ‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

Wasu da ake zargin ‘Yan Ta’adda ne sun yiwa Asibitin Koyar na Jami’ar Jihar Osun dake garin Osogbo tsinke, domin daukar gawar guda cikin abokan ayyukan ta’addanci su da ya mutu sakamako Harbin bindiga.

An ruwaito cewa mutum 2 ne suka mutu sakamakon harin na ‘yan bindigar a ranar talata a garin na Osogbo, sai dai jami’an tsaro na Amotekun sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Daban.

Daga bisani wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun lalata gidan kwamandan Amotekun, Amitolu Shittu, a yayin artabun ne guda cikin su ya sami raunukan Harbin bindiga kuma an kai shi asibitin koyarwa na UNIOSUN domin yi masa magani daga bisani yace mutu.

Majiyar mu ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye asibitin ne da nufin dauko gawar abokin aikinsu amma jami’an kiwon lafiya suka dage kan a basu cikakkun takardu, wanda ‘yan ta’addan suka yi biris da bukatar jami’an asibitin.

Wani shaidar gani da Ido yace, ‘yan ta’addan sun kara karfi inda suka kutsawa cikin harabar Asibitin da muggana makamai da suka hadar da Gatari, Katako, Wukake da dai sauran makamai masu razanarwa, wannan ta sanya jami’an asibitin rufe manyan kofofin asibitin na tsawon sa’oi 2 abinda ya hana su dauke gawar.

Likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aiktan asibitin sun nemi mafaka kafin jami’an tsaro su shiga Tsakani.

Shugaban kwamitin ba da shawara a Asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Osun, Osogbo, Babatunde Afolabi ya tabbatar da faruwar lamarin amma y ace ‘an shawo kan matsalar; bayan sun gudanar da bincike kan gawar an fitar da ita domin binne wa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp