Home Labarai ‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

‘Yan Ta’adda Sun Afka Asibitin UNIOSUN Domin Kwato Gawar Dan Uwansu

Wasu da ake zargin ‘Yan Ta’adda ne sun yiwa Asibitin Koyar na Jami’ar Jihar Osun dake garin Osogbo tsinke, domin daukar gawar guda cikin abokan ayyukan ta’addanci su da ya mutu sakamako Harbin bindiga.

An ruwaito cewa mutum 2 ne suka mutu sakamakon harin na ‘yan bindigar a ranar talata a garin na Osogbo, sai dai jami’an tsaro na Amotekun sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Daban.

Daga bisani wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun lalata gidan kwamandan Amotekun, Amitolu Shittu, a yayin artabun ne guda cikin su ya sami raunukan Harbin bindiga kuma an kai shi asibitin koyarwa na UNIOSUN domin yi masa magani daga bisani yace mutu.

Majiyar mu ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye asibitin ne da nufin dauko gawar abokin aikinsu amma jami’an kiwon lafiya suka dage kan a basu cikakkun takardu, wanda ‘yan ta’addan suka yi biris da bukatar jami’an asibitin.

Wani shaidar gani da Ido yace, ‘yan ta’addan sun kara karfi inda suka kutsawa cikin harabar Asibitin da muggana makamai da suka hadar da Gatari, Katako, Wukake da dai sauran makamai masu razanarwa, wannan ta sanya jami’an asibitin rufe manyan kofofin asibitin na tsawon sa’oi 2 abinda ya hana su dauke gawar.

Likitoci da ma’aikatan jinya da sauran ma’aiktan asibitin sun nemi mafaka kafin jami’an tsaro su shiga Tsakani.

Shugaban kwamitin ba da shawara a Asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Osun, Osogbo, Babatunde Afolabi ya tabbatar da faruwar lamarin amma y ace ‘an shawo kan matsalar; bayan sun gudanar da bincike kan gawar an fitar da ita domin binne wa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp