Home Labarai Farfesa Gwarzo Ya Tallafawa Dalibin Nijeriya A Rasha Da Naira MIliya Daya

Farfesa Gwarzo Ya Tallafawa Dalibin Nijeriya A Rasha Da Naira MIliya Daya

Wanda ya assasa Jami’ar Maryam Abacha wato Maryam Abacha American University (MAAUN) Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya bada tallafi naira miliyan 1 ga hazikin dalibin likitanci Usman Yahya, wanda ke tsare a hannun hukumar Shige da ficcen kasar Rasha.

Makwanin 2 da suka gabata Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa Yahaya wanda ya cibiyar Nazarin Kimiyya ta kasar Rasha ta karrama da lambar yabo matsayin Dalibin Likitanci mafi hazaka, a Jami’ar Jihar Irkutsk (ISMU), hukumar makarantar ta fara dakatar dashi daga shiga dakin kwanan Dalibai a harabar Jami’ar, sakamakon kin biyan masa kudin makaranta da gwamnatin jihar Sokoto tayi.

Tallafin zunzuruntun kudin da Farfesa Gwarzo ya bayar, wanda kungiyar Daliban Nijeriya a kasashen Turai ta karbar, ya biyo ta hannun Manajan Jaridar PRNigeria dake jihar Kano, Adnan Mukhtar.

A cewar Gwarzo, akwai bukatar ‘yan Nijeriya masu kishin kasar da su gaggauta kai dauki ga Yahaya, don tabbatar da ganin ya cimma burinsa na rayuwa daya sanya a gaba.

“Makomar Usman Yahaya tana cikin hadari, dole ne mu yi wani abu don tabbatar da cewa ya cigaba da karatun sa, tare da karbo shi daga hannun hukumomin kasar Rasha, haka zalika wannan kudi naira miliyan 1 dana bayar ta hannun kungiyar ANSE zata taimaka, kuma muna sa rana akwai gudunmawa daga wajen masu hannu da shuni na Nijeriya wadda zata taimaka wajen cire Yahaya daga halin da yake cike a halin yanzu.

Da yake bayani dangane da wannan tallafi da Farfesa Gwarzo ya bayar, shugaban kungiyar Daliban ta ANSE, ya sake yin kira ga gwamnatin jihar Sokoto da ta yi Adalci gami da jinkan ga Yahaya, tare da gaggauta taimakawa wajen magance matsalolin da yake ciki a kasar ta Rasha.

“Ba mu da bakin da zamu godewa Farfesa Gwarzo, domin ya taimaka matuka a kokarin da muke na ceto Usman Yahaya, don haka muna fata sauran Attajirai da masu hannun da Shuni su yi koyi da shi,” Inji Shi.

Usman Yahaya dai ya shiga cikin halin kakanakayin ne bayan da hukumar Jami’ar ta kore shi daga cikin harabarta, sakamakon wasu ayyukan cin hanci da Rashawa a hukumar bada tallafin karatu ta jihar Sokoto, da ake zargi ya haifar da jan kafa a wajen biya masa kudin karatu, hukumomin shige da fice sun tsare shi a sansani sun a Angarsk Irkutsk.

An dai zargi wani jami’in hukumar ba da tallafin karatu ta jihar Sokoto ne ke da hannu a wannan ta’asa, wanda ya kwashe makudan kudaden daga cikin kudaden tallafin karatu na daliban kasashen waje da Gwamnatin jihar Sokoto ta amince a fitar duk shekara, tun daga shekarar 2016.

Yahaya ya bayyana sau 2 a gaban wata kotun kasar Rasha, kuma idan aka same shi da laifi za’a iya korar shi daga Jami’ar ta ISMU, tare da tsare shi, koma a haramta masa shiga kasar ta Rasha.

Ko da PRNigeria ta tuntubi sashen hulda da dalibai na Jami’ar, Ms Elena Orel tace hukumar Jami’ar bata tsare dalibin da karfi ba karfi ba domin ta wulakan ta shi.

Tace kawai an kori Yahaya daga wajen zaman dalibai ne sakamakon karya dokokin shige da fice na kasar, wato rashin cikakkun takardu.

“An kai shi sansanin shige da fice domin samun damar gyara bisa ko sabuntata, babu wani nau’i na wulakanci ko cin zarafi daga hukumar, dalibin yana da damar gudanar da al’amurra  sa cikin ‘yanci.

“Duk da haka, bayan samun wasika daga masu daukar nauyinsa daga jihar Sokoto a Nijeriya, a halin yanzu dalibin yana can a masaukin jami’ar domin kare lafiyar sa.

“amma idan a karshe dalibin ya kasa sabunta takardunsa, babu shakka ana iya fitar da shi daga masaukin daliban.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp