Home SIYASA Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

Okowa and Atiku

Daga Karshe, Atiku ya Zaɓi Okowa a Matsayin Abokin Tafiyarsa

 

‘Dan takarar shugabancin kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana Gwamna Ifeanyi Okowa matsayin abokin tafiyarsa.

Duk da kwamitin shawari ta zabi Gwamna Wike na jihar Ribas, an gano cewa Atiku ya sakankance cewa Wike bayan kaunarsa.

Har ila yau, wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP, ba su aminta da Gwamna Wike ba ganin irin kusancin da kujerar take da ta shugaban kasa.

FCT, Abuja – Atiku Abubakar, ‘dan takarar shugabancin kasa karkashin jam’iyyar PDP, ya zabi Ifeanyi Okowa, gwamnan jihar Delta a matsayin abokin tafiyarsa a zaben 2023 mai gabatowa.

Kwamitin gudanar da ayyuka na jam’iyyar PDP a ranar Laraba ya zabi Nyesom Wike, gwamnan jihar Ribas, a matsayin wanda zai kasance mataimakin ‘dan takarar shugabancin kasan.

Mambobin NWC sun yi zabe inda Wike ya samu kuri’u 13 yayin da Okowa ya samu uku kacal, lamarin da yasa masu ruwa da tsakin suka aminta da Wike.

Sai dai, Atiku Abubkar na gano ya kasa sakin jiki da Wike a matsayin abokin tafiyarsa sabodaya sakankance cewa gwamnan baya kaunarsa.

Wike yayi wa Aminu Waziri Tambuwal aiki a zaben fidda gwani na 2019, duk da kuwa cewa Atiku ya zo ya lashe zaben, Arise Tv ta ruwaito.

Wasu manya a PDP an gano ba su aminta da Wike ba saboda tsananin kusancin mataimakin shugaban kasa da kujerar shugabancin kasan.

Ya sanar da zabinsa ne a ranar Alhamis a hedkwatar jam’iyyar PDP ta lasa dake Abuja. Ya ce ya yanke wannan shawarar ne bayan dogon nazari da tattaunawa da masu ruwa da tsakin jam’iyyar.

A cewarsa, hukunci ne mai tsauri gare shi wurin yankewa duba da irin nagartattun mutanen da aka shawarcesa ya zaba daga ciki. “Ina farin cikin sanar da sunan Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakin ‘dan takarar shugaban kasa.

Ina hango tafiyar da kasar mu, tare da dukkan ‘yan Najeriya da kuma gina zaman lafiya, hadin kai da cigaba ga kowa,” ya wallafa a shafinsa na Twitter.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp