Home Labarai BINCIKE: Shin Gaskiya Ne Tsakanin Shekarar 2010 Zuwa 2018 An Yi Tikitin...

BINCIKE: Shin Gaskiya Ne Tsakanin Shekarar 2010 Zuwa 2018 An Yi Tikitin Kirista – Kirista A Jihar Ekiti?

KORAFI: Akwai wani rubutu dake yawo a kafafen sada zumunta na zamani (Facebook) cewa a jihar Ekiti an yi tikitin Kirista – Kirista daga shekarar 2010 – 2018.

CIKAKKEN BAYANI: A cikin wani shafin facebook; mai Suna Buharist Reporter, an wallafa wani rubutu a ranar 30 ga watan Yuni, wanda ke kunshe da jerin jadawalin ‘yan siyasar da suka gabata wadanda suka taba yin takarar shugabancin Nijeriya ko kuma gwamna a wata jihar da suka dauki mataimakin su daga cikin mabiya Addini Kirista, rubutun da aka yiwa lakabi da “FLASHBACK CHRISTIAN-CHRISTIAN TICKET”  ya Ambato sunan Mista Ayo Fayose wanda ya Mulki jihar Ekiti daga shekarar 2014 zuwa 2018 tare da mataimakin sa, Niyi Adebayo, tikitin Kirista-kirista ne amma Al’ummar Musulmi basu ce komai kan lamarin ba.

Haka kuma shafin ya mabato sunan Gwamna Kayode Fayemi na Ekiti tsakanin shekara 2010 zuwa 2014 ya dauki kirista a matsayin mataimaki sa.

BINCIKEN TABBATARWA: PRNigeria  ta gudanar da wani bincike da ya tabbatar mata da cewa Dr. Kayode Fayemi da Mr Ayo Fayose sun gudanar da tikitin kirista – kirista a yayin da suke takarar zaman gwamnan jihar kuma bayan gudanar da zaben sun sami nasarar.

A tsakanin shekarar 2010 zuwa 2014, Dr Kayode Fayemi ya dauki Kirista a matsayin wanda zai masa mataimaki, Funmilayo Olayinka karkashin Inuwar jam’iyyar (ACN), wanda daga bisani ya mutu a ranar 6 ga watan Afrilun 2013.

Ta cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 3 ga watan Mayu, shekarar 2013, yayin da yake jawabi ga kakakin majalisar dokokin jihar Adewale Omiri, ya bukaci majalisar ta aminci da nadin farfesa Modupe Adelabu, wanda shima mabiyin addinin kirista ne, matsayin mataimakin Gwamnan jihar, domin cike gurbin mataimakin gwamnan jihar da ya mutu.

Haka kuma Ayo Fayose ya gudanar da tikitin kirista-kirista tsakanin shekarar 2014 zuwa 2018 a karkashin inuwar jam’iyyar “People Democratic Party” PDP. Inda ya dauki Farfesa Kolapo Olusola Eleka, wanda shima mabiyin addinin kiristanci ne.

KAMMALAWA: Sakamakon bayanan da PRNigeria ta tattara a jihar ya tabbatar mata da cewa Mista Ayo Fayose da Dr. Kayode Fayemi sun gudanar da tikitin Kirista-kirista a mabambanta lokaci a jihar ta Ekiti.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp