Home Labarai BINCIKE: Shin Gaskiya Ne Tsakanin Shekarar 2010 Zuwa 2018 An Yi Tikitin...

BINCIKE: Shin Gaskiya Ne Tsakanin Shekarar 2010 Zuwa 2018 An Yi Tikitin Kirista – Kirista A Jihar Ekiti?

KORAFI: Akwai wani rubutu dake yawo a kafafen sada zumunta na zamani (Facebook) cewa a jihar Ekiti an yi tikitin Kirista – Kirista daga shekarar 2010 – 2018.

CIKAKKEN BAYANI: A cikin wani shafin facebook; mai Suna Buharist Reporter, an wallafa wani rubutu a ranar 30 ga watan Yuni, wanda ke kunshe da jerin jadawalin ‘yan siyasar da suka gabata wadanda suka taba yin takarar shugabancin Nijeriya ko kuma gwamna a wata jihar da suka dauki mataimakin su daga cikin mabiya Addini Kirista, rubutun da aka yiwa lakabi da “FLASHBACK CHRISTIAN-CHRISTIAN TICKET”  ya Ambato sunan Mista Ayo Fayose wanda ya Mulki jihar Ekiti daga shekarar 2014 zuwa 2018 tare da mataimakin sa, Niyi Adebayo, tikitin Kirista-kirista ne amma Al’ummar Musulmi basu ce komai kan lamarin ba.

Haka kuma shafin ya mabato sunan Gwamna Kayode Fayemi na Ekiti tsakanin shekara 2010 zuwa 2014 ya dauki kirista a matsayin mataimaki sa.

BINCIKEN TABBATARWA: PRNigeria  ta gudanar da wani bincike da ya tabbatar mata da cewa Dr. Kayode Fayemi da Mr Ayo Fayose sun gudanar da tikitin kirista – kirista a yayin da suke takarar zaman gwamnan jihar kuma bayan gudanar da zaben sun sami nasarar.

A tsakanin shekarar 2010 zuwa 2014, Dr Kayode Fayemi ya dauki Kirista a matsayin wanda zai masa mataimaki, Funmilayo Olayinka karkashin Inuwar jam’iyyar (ACN), wanda daga bisani ya mutu a ranar 6 ga watan Afrilun 2013.

Ta cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 3 ga watan Mayu, shekarar 2013, yayin da yake jawabi ga kakakin majalisar dokokin jihar Adewale Omiri, ya bukaci majalisar ta aminci da nadin farfesa Modupe Adelabu, wanda shima mabiyin addinin kirista ne, matsayin mataimakin Gwamnan jihar, domin cike gurbin mataimakin gwamnan jihar da ya mutu.

Haka kuma Ayo Fayose ya gudanar da tikitin kirista-kirista tsakanin shekarar 2014 zuwa 2018 a karkashin inuwar jam’iyyar “People Democratic Party” PDP. Inda ya dauki Farfesa Kolapo Olusola Eleka, wanda shima mabiyin addinin kiristanci ne.

KAMMALAWA: Sakamakon bayanan da PRNigeria ta tattara a jihar ya tabbatar mata da cewa Mista Ayo Fayose da Dr. Kayode Fayemi sun gudanar da tikitin Kirista-kirista a mabambanta lokaci a jihar ta Ekiti.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp