Home Labarai Ba za mu Lamunta da Hare-Haren da ake Kai wa Jami’an ‘Yan...

Ba za mu Lamunta da Hare-Haren da ake Kai wa Jami’an ‘Yan Sanda ba – IG Baba Alkali

Ba za mu Lamunta da Hare-Haren da ake Kai wa Jami’an ‘Yan Sanda ba – IG Baba Alkali

 

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba, psc(+), NPM, fdc, ya yi kakkausar suka kan yadda ake ci gaba da kai hare-hare kan jami’an ‘yan sanda da wasu mutane sanye da kayan aiki, suna gudanar da ayyukan hukuma da na doka a wurare daban-daban a fadin kasar nan. IGP din ya jaddada cewa hare-haren da ake kaiwa Jami’an ‘Yan Sanda, wadanda ke sanye da rigar kakin jihar, duk ya sabawa doka, kuma cin zarafi ne da bin doka da oda.

IGP ya yi gargadin cewa, ba za a sake lamuntar kai wa jami’an ‘yan sanda da mutanen da ke bakin aikinsu hari ba, ta kowace hanya, domin rundunar ta rike rayukan ma’aikatanta. Don haka, IGP ya umurci dukkan hukumomin ‘yan sanda da su tabbatar da cewa mutanen da ke kai farmaki kan jami’an ‘yan sanda, ba tare da la’akari da abubuwan da suka gabata ba, sun fuskanci fushin doka ta hanyar gaggawar gurfanar da su a gaban kotunan da suka cancanta.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan a yayin da yake nanata kudirin rundunar na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi, ya jaddada muhimmancin bin muhimman hakkokin jami’an ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro, domin ba su damar ci gaba da aikinsu na alfarma. da kuma kare ‘yan kasa da kyau da kiyaye doka da oda.

CSP OLUMUYIWA ADEJOBI, mnipr, mipra, Jami’in Hulda da Jama’a na

FORCE

FORCE HEADQUARTERS

ABUJA

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp