Home Labarai Yadda Sojoji Suka yi wa ‘Yan Bindiga kwanton Bauna a Hanyar Kaduna-Zaria

Yadda Sojoji Suka yi wa ‘Yan Bindiga kwanton Bauna a Hanyar Kaduna-Zaria

Yadda Sojiji Suka yi wa ‘Yan Bindiga kwanton Bauna a Hanyar Kaduna-Zaria

Dakarun sojin Najeriya sun fatattaki ‘yan bindiga a kewayen yankin Fondisho general, kan hanyar Kaduna zuwa Zaria a karamar hukumar Igabi.

A wani martani da gwamnatin jihar Kaduna ta bayar, an bayyana cewa, sojojin da suka yi gaggawar mayar da martani ga sahihan bayanan sirri, sun yi kwanton bauna a wurin.

Da shiga yankin ne ‘yan bindigar suka yi wa ‘yan kwanton baunar kwanton bauna, inda suka yi ta harbe-harbe a yayin da dakarun suka fatattake su da kakkausar murya. Biyu daga cikin masu laifin an kashe su.

Gwamnatin jihar Kaduna ta samu gamsuwa, sannan ta yabawa sojojin bisa gaggawar da suka yi wajen amsa rahotannin sirri.

Gwamnati ta mika godiyarta ga sojoji da sauran jami’an tsaro, tare da karfafa musu gwiwa da su ci gaba da kokarin da suke yi na murkushe duk wasu masu aikata laifuka.

Tunda da yawa daga cikin ‘yan bindigar sun tsere da raunukan harbin bindiga, gwamnati ta yi kira ga al’ummomin yankin baki daya da su kai rahoton duk wani mutum da ake zargi da ke neman kulawar lafiya. Za a iya samun dakin aikin tsaro ta 09034000060 da 08170189999.

Za a ci gaba da sintiri da makamai a yankin baki daya.

Sa hannu

Samuel Aruwan

Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp