Home Labarai Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a...

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

 

A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan kungiyar Civilian Joint Task Force suka dakile wani hari da suka kai wani gari a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina tare da kashe wasu ‘yan ta’adda biyu.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma cafke wasu ‘yan ta’adda biyar tare da kame babura tara da aka yi amfani da su wajen kai harin.

Wasu majiyoyi da suka zanta da wakilinmu sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari garin ne da misalin karfe 4:30 na yamma, inda suka ce ‘yan ta’addan sun mamaye garin ne a cikin babura akalla 10.

A yayin farmakin, tawagar da ke yaki da ‘yan ta’addan sun yi arangama da ‘yan ta’addan, kuma a yayin musayar wuta da bindiga, sun kashe mutane tara da ake zargi.

Rahotanni sun bayyana cewa rundunar ta kama wasu ‘yan kungiyar su biyar a yayin samamen.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya ce har yanzu DPO da ke yankin bai yi wa rundunar bayanin faruwar lamarin ba.

Isah ya ce, “Zan yi muku bayani a duk lokacin da DPO na yankin ya sanar da hukumar game da lamarin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp