Home Labarai Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a...

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

 

A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan kungiyar Civilian Joint Task Force suka dakile wani hari da suka kai wani gari a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina tare da kashe wasu ‘yan ta’adda biyu.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma cafke wasu ‘yan ta’adda biyar tare da kame babura tara da aka yi amfani da su wajen kai harin.

Wasu majiyoyi da suka zanta da wakilinmu sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari garin ne da misalin karfe 4:30 na yamma, inda suka ce ‘yan ta’addan sun mamaye garin ne a cikin babura akalla 10.

A yayin farmakin, tawagar da ke yaki da ‘yan ta’addan sun yi arangama da ‘yan ta’addan, kuma a yayin musayar wuta da bindiga, sun kashe mutane tara da ake zargi.

Rahotanni sun bayyana cewa rundunar ta kama wasu ‘yan kungiyar su biyar a yayin samamen.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya ce har yanzu DPO da ke yankin bai yi wa rundunar bayanin faruwar lamarin ba.

Isah ya ce, “Zan yi muku bayani a duk lokacin da DPO na yankin ya sanar da hukumar game da lamarin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp