Home Labarai Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan...

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

Bala mohammed

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

 

AREWA AGENDA – Kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Bauchi CAN ta yi Allah wadai da yunkurin wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su wanene ba na yunkurin kashe babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Bauchi kan harkokin addinin Kirista Fasto Zakka Magaji.

Shugaban kungiyar CAN reshen Bauchi, Rabaran Dr Abraham Damina Dimeus ya bayyana haka a lokacin da ya jagoranci jami’an kungiyar a ziyarar jaje a gidan hadimin gwamnan da ke Birshi, al’ummar da ke wajen birnin Bauchi.

Ya ce harin ba abin da ya dace ba kuma abin takaici ne, yana mai cewa ya kamata mutane su sani cewa rayuwa abu ne mai tsarki kuma dole ne a kiyaye ta ko ta halin kaka.

Shugaban kungiyar ta CAN wanda ya yi godiya ga Allah da cewa ba a samu asarar rai ba yayin harin kamar yadda ba a yi garkuwa da kowa ba, ya jaddada bukatar karfafa tsaro a fadin kasar nan.

Ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da abin ya shafa musamman a jihar da ma kasar baki daya da su gaggauta daukar matakan tsaro musamman a yankunan da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake yabawa gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamnan jihar Sen Bala Mohammed Abdulkadir bisa kokarin da take yi na kare rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, ya ce za a iya kara kaimi kan lamarin.

Abraham Damina ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu lura da tsaro da kuma sa kai wajen bada bayanai game da miyagun qwai a cikin al’umma domin a ci gaba da samun zaman lafiya a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp