Home Labarai Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan...

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

Bala mohammed

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

 

AREWA AGENDA – Kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Bauchi CAN ta yi Allah wadai da yunkurin wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su wanene ba na yunkurin kashe babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Bauchi kan harkokin addinin Kirista Fasto Zakka Magaji.

Shugaban kungiyar CAN reshen Bauchi, Rabaran Dr Abraham Damina Dimeus ya bayyana haka a lokacin da ya jagoranci jami’an kungiyar a ziyarar jaje a gidan hadimin gwamnan da ke Birshi, al’ummar da ke wajen birnin Bauchi.

Ya ce harin ba abin da ya dace ba kuma abin takaici ne, yana mai cewa ya kamata mutane su sani cewa rayuwa abu ne mai tsarki kuma dole ne a kiyaye ta ko ta halin kaka.

Shugaban kungiyar ta CAN wanda ya yi godiya ga Allah da cewa ba a samu asarar rai ba yayin harin kamar yadda ba a yi garkuwa da kowa ba, ya jaddada bukatar karfafa tsaro a fadin kasar nan.

Ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da abin ya shafa musamman a jihar da ma kasar baki daya da su gaggauta daukar matakan tsaro musamman a yankunan da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake yabawa gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamnan jihar Sen Bala Mohammed Abdulkadir bisa kokarin da take yi na kare rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, ya ce za a iya kara kaimi kan lamarin.

Abraham Damina ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu lura da tsaro da kuma sa kai wajen bada bayanai game da miyagun qwai a cikin al’umma domin a ci gaba da samun zaman lafiya a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp