Home Labarai Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan...

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

 

AREWA AGENDA – Kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Bauchi CAN ta yi Allah wadai da yunkurin wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su wanene ba na yunkurin kashe babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Bauchi kan harkokin addinin Kirista Fasto Zakka Magaji.

Shugaban kungiyar CAN reshen Bauchi, Rabaran Dr Abraham Damina Dimeus ya bayyana haka a lokacin da ya jagoranci jami’an kungiyar a ziyarar jaje a gidan hadimin gwamnan da ke Birshi, al’ummar da ke wajen birnin Bauchi.

Ya ce harin ba abin da ya dace ba kuma abin takaici ne, yana mai cewa ya kamata mutane su sani cewa rayuwa abu ne mai tsarki kuma dole ne a kiyaye ta ko ta halin kaka.

Shugaban kungiyar ta CAN wanda ya yi godiya ga Allah da cewa ba a samu asarar rai ba yayin harin kamar yadda ba a yi garkuwa da kowa ba, ya jaddada bukatar karfafa tsaro a fadin kasar nan.

Ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da abin ya shafa musamman a jihar da ma kasar baki daya da su gaggauta daukar matakan tsaro musamman a yankunan da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake yabawa gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamnan jihar Sen Bala Mohammed Abdulkadir bisa kokarin da take yi na kare rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, ya ce za a iya kara kaimi kan lamarin.

Abraham Damina ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu lura da tsaro da kuma sa kai wajen bada bayanai game da miyagun qwai a cikin al’umma domin a ci gaba da samun zaman lafiya a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp