Home Labarai Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar...

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

 

AREWA AGENDA – A kalla mutane 10 ne suka mutu yayinda wasu 236 suka kamu da cutar kwalara a jihar Gombe.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Gombe, Dakta Abdulrahman Shuaibu, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake zantawa da manema labarai a madadin Kwamishinan Lafiya, Dakta Habu Dahiru, kan bullar cutar a jihar.

Ya ce a ranar 20 ga Satumba, 2022, adadin wadanda suka kamu da cutar ya kai 236, inda ya ce a shekarar 2021, jihar ta samu adadin mutane 2,373 a cikin bullar cutar guda uku a shekarar da ta gabata.

“A wannan shekarar, daga ranar 30 ga watan Yuni, 2022, mun samu bullar cutar kwalara a karamar hukumar Balanga, kuma saboda shiri da gaggawar da aka yi, an shawo kan ta sosai ba tare da wani tashin hankali ba.

“Muna ganin yadda ruwan sama ya kara kamari, wanda ya haifar da ambaliya a sassan jihar da dama kuma hakan ya haifar da bullar cutar kwalara a Unguwani takwas da ke fadin kananan hukumomin Balanga, Yamaltu-Deba, Nafada, Funakaye da Gombe.

“Ma’aikatar Lafiya ta Jiha ta fara aiwatar da ayyukan kiwon lafiyar jama’a cikin gaggawa don rigakafi da shawo kan cutar kwalara. Ya zuwa jiya, 20 ga Satumba, 2022, an samu karuwar masu dauke da cutar a jihar Gombe, ya zuwa yanzu an jera masu kararraki 236.” Inji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp