Home Labarai Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar...

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

 

AREWA AGENDA – A kalla mutane 10 ne suka mutu yayinda wasu 236 suka kamu da cutar kwalara a jihar Gombe.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Gombe, Dakta Abdulrahman Shuaibu, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake zantawa da manema labarai a madadin Kwamishinan Lafiya, Dakta Habu Dahiru, kan bullar cutar a jihar.

Ya ce a ranar 20 ga Satumba, 2022, adadin wadanda suka kamu da cutar ya kai 236, inda ya ce a shekarar 2021, jihar ta samu adadin mutane 2,373 a cikin bullar cutar guda uku a shekarar da ta gabata.

“A wannan shekarar, daga ranar 30 ga watan Yuni, 2022, mun samu bullar cutar kwalara a karamar hukumar Balanga, kuma saboda shiri da gaggawar da aka yi, an shawo kan ta sosai ba tare da wani tashin hankali ba.

“Muna ganin yadda ruwan sama ya kara kamari, wanda ya haifar da ambaliya a sassan jihar da dama kuma hakan ya haifar da bullar cutar kwalara a Unguwani takwas da ke fadin kananan hukumomin Balanga, Yamaltu-Deba, Nafada, Funakaye da Gombe.

“Ma’aikatar Lafiya ta Jiha ta fara aiwatar da ayyukan kiwon lafiyar jama’a cikin gaggawa don rigakafi da shawo kan cutar kwalara. Ya zuwa jiya, 20 ga Satumba, 2022, an samu karuwar masu dauke da cutar a jihar Gombe, ya zuwa yanzu an jera masu kararraki 236.” Inji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp