Home Labarai Matashi ya Kashe Abokinsa da Wuka Akan Abinci a Legas

Matashi ya Kashe Abokinsa da Wuka Akan Abinci a Legas

Matashi ya Kashe Abokinsa da Wuka Akan Abinci a Legas

 

Wani matashi mai suna Daniel Akindele ya daba wa abokinsa Ayo Bameke wuka har lahira a lokacin da suke fafata rikici kan abinci a Abattoir Complex da ke unguwar Agege a jihar Legas.

An tattaro cewa, Akindele da Bameke, tare da wasu abokai, sukan ziyarci rukunin domin buga kwallon kafa.

A ranar da lamarin ya faru, wakilinmu ya samu labarin cewa ‘yan biyun da abokansu sun ziyarci rukunin gidajen kamar yadda suka saba.

An ce Bameke ya bar abokansa ne don sayan abinci.

Daga baya ya dawo ya gana da abokansa a harabar gidan, aka ce yana cin abinci, sai Akindele, wanda shi ma yana jin yunwa, ya bukaci a raba abincin.

An ba da rahoton cewa bukatar ta haifar da cece-kuce da ta rikide zuwa kaka-nika-yi tsakanin abokanan biyu.

A yayin rikicin da ya barke a gaban Harmony Abattoir Management Services Limited, Bameke ya yi amfani da almakashi wajen raunata Akindele.

Wani jami’in tsaro na kamfanin, Segun Ijaola, a lokacin da yake zantawa da wakilinmu a ziyarar da ya kai wurin, ya ce Akindele ya yi galaba a kan Bameke, inda ya tattara almakashi, sannan ya daba masa wuka a kirji.

Ya ce, “matasan adadinsu hudu ne kuma tsakanin shekaru 14 zuwa 15. Kullum suna tare. Da misalin karfe 11 na safiyar ranar Asabar, sun kasance a gaban Harmony Abattoir Management Services Limited. Wata ma’aikaciyar mu tana kan hanyarta ta fito ta dauko wani abu a falon sai ta ga daya daga cikin yaran (Bameke) kwance a kasa.

“A yayin da take kokarin sanin abin da ke damun yaron, sai ta kira abokanan ukun su tambayi abin da ya faru. Ana cikin haka ne ta gano cewa an caka ma Bameke almakashi na haihuwa a gefen hagu na kirjinsa. Bayan da Akindele ya fahimci cewa Bameke na kwance babu motsi a kasa, sai ya yi kokarin tserewa amma matar ta kama shi.

“Yayin da yake yi masa tambayoyi, Akindele ya fara ikirari. Ya ce Bameke shi ne ya yi amfani da almakashi ya yanke hannunsa kafin ya tattara almakashin ya caka masa gefen hagu na kirjinsa. Nan take ma’aikatan kamfaninmu suka garzaya da Bameke asibitin Merit da ke Agege, amma likitan ne ya tabbatar da mutuwarsa. An kai gawar zuwa dakin ajiyar gawa.”

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Hundeyin ya ce, “An gurfanar da Akindele a gaban Kotun Majistare ta Yaba, Legas, a ranar 13 ga Satumba, 2022, kan zargin kisan kai. Alkalin kotun ya ba da umarnin a tsare matashin daga baya.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp