Home Labarai Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da lokacin bukukuwan maulidu wajen yiwa kasar Addu’ar kan matsalolin tsaron da suka addabi Al’ummar ta.

Wannna na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga Ministan tsaron Nijeriya Manjo Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya, kan harkokin sadarwa Mohammad Abdulkadri ya fitar domin taya Al’ummar Musulmi murnar Mauludin Fiyayyen Halitta na bana.

Yace haihuwar fiyayyen halitta ta zo wa da duniya da abubuwan da suka jibanci yadda za’ayi koyi da hakuri, addu’oi da Kankan da kai, gami da tsoron Allah, wadanda a cewar sa sun cancanci koyi ga dukkan musulmi da wadanda ba musulmi ba.

Ministan tsaron ya bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da wanna biki wajen rokowa kasar kyakkyawar makoma, ta hanyan yi mata add’oin samun zaman lafiya mai dorewa, gami da kasancewa cikin masu bada gudunmawar da ta dace wajen magance kalubalen tsaron da kasar ke fama da shi, tare da shiga cikin masu samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, wanda shine tushen addinin Musulunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp