Home Labarai Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da lokacin bukukuwan maulidu wajen yiwa kasar Addu’ar kan matsalolin tsaron da suka addabi Al’ummar ta.

Wannna na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga Ministan tsaron Nijeriya Manjo Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya, kan harkokin sadarwa Mohammad Abdulkadri ya fitar domin taya Al’ummar Musulmi murnar Mauludin Fiyayyen Halitta na bana.

Yace haihuwar fiyayyen halitta ta zo wa da duniya da abubuwan da suka jibanci yadda za’ayi koyi da hakuri, addu’oi da Kankan da kai, gami da tsoron Allah, wadanda a cewar sa sun cancanci koyi ga dukkan musulmi da wadanda ba musulmi ba.

Ministan tsaron ya bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da wanna biki wajen rokowa kasar kyakkyawar makoma, ta hanyan yi mata add’oin samun zaman lafiya mai dorewa, gami da kasancewa cikin masu bada gudunmawar da ta dace wajen magance kalubalen tsaron da kasar ke fama da shi, tare da shiga cikin masu samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, wanda shine tushen addinin Musulunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp