Home DUNIYA Harin Al-Shabab yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 9 tare da Jikkata 47 a...

Harin Al-Shabab yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 9 tare da Jikkata 47 a Somalia

Rahotanni na bayyana cewa Akalla mutane 9 aka kashe, tare da jikkata wasu 47 sakamakon harin kan wani Otal da ke birnin Kismaayo a kudancin Somalia, farmakin da kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakinsa a ranar Lahadi.

Birnin na Kisimaayo mai tashar jiragen ruwa shi ne na baya-bayan nan da ya fuskanci hare-haren kungiyar Al Shebaab mai alaka da Al-Qaeda, wadda ta fi mayar da hankali wajen kai hare-hare a birnin Mogadishu da kuma yankin tsakiyar kasar Somalia.

Bayanai sun ce, mayakan na Al Sheebaab sun kaddamar da harin na ranar Lahadi ne da misalin karfe 12:45 na rana wato 9:45 na safe agogon GMT, lokacin da wata mota makare da bama-bamai ta afkawa kofar shiga Otal din Tawakal. Sai kuma da aka shafe sa’o’i shidda kafin jami’an tsaro su kashe mahara uku da suka kai farmakin, yayin da ragowar guda ya tarwatsa damarar bam din da ke jikinsa.

Ministan tsaron yankin Jubaland Yusuf Hussein Osman ya shaida wa manema labarai cewa, daga cikin wadanda suka jikkata a harin akwai daliban da suka tashi daga wata makaranta da ke kusa da inda aka kai farmakin.

‘Yan sandan Somalia sun ce fararen hula ne suka fi mu’amala da Otal din da aka kaiwa hari, sai dai kungiyar Al-Shabaab ta ce mambobin gwamnatin yankin Jubaland, inda birnin Kismayo yake, suna ganawa cikin Otal din, a lokacin da mayakanta suka kai farmakin na sa’o’i 6.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp