Home General Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan...

Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna

Za’a girke Jami’an ‘yan sanda, biyo bayan dawo da jigilar fasinjoji a jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na kasa CSP Olumuyiwa Adejobi, mnipr, mipra ya fitar a birnin tarayyar kasar Abuja mai dauke da kwanan watan 4 ga watan Disamba 2022 da aka akewa PRNigeria.
Sanarwar tace babban sefeton ‘Yan sanda Nijeriya Usman Alkali Baba, psc(+), NPM, NEAPS, fdc, CFR, ya bada umarnin girki Jami’an kwantar da tarzoma na Mobile Force, K-9, Force na kwarru da kuma Jami’an ‘yan sandan layin dogo domin gudanar da ayyukan tsaro kan hanyar jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna ranar litinin 5 ga Disambar 2022.
Inda sanarwa ta kara da cewa Rundunar ‘yan sandan Nijeriya na cigaba da tattaunawa da hukumar dake lura da Jiragen Kasan Nijeriya da sauran Jami’an tsaro domin gudanar da aikin tsaron Al’umma yadda ya kamata.
Dakarun zasu lura da muhimman wuraren na tashar jirgin kasar da hanyar da yake bi da kuma bada shawarwari don samar da ingantacce tsaro ga fasinjoji da dukiyoyin su ta hanyar kare su ga dukkan abinda kaje kazo
Babban Sifeton ‘yan sanda ya kuma tabbarwa da Al’umma kasar musamman fasinjojin jirgin kasar cewa zasu kare su da lafiyar su da dukiyar su da zarar sun hau kan hanya domin yin balaguro, dama sauran fasinjojun dake kan jirgin kasa a dukkan fadin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp