Home General Dakarun sojojin Nijeriya sun Murkushe ‘Yan Ta’adda a Mafa ta Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun Murkushe ‘Yan Ta’adda a Mafa ta Jihar Borno

Dakarun sojin Nijeriya karkashin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) a Arewa Maso Gabas sun sami Nasarar tarwatsa gungun ‘Yan Boko Haram a wani kwanton Bauna da suka yi musu a kauyen
Troops of Operation kauyen Ngowom dake karamar Hukumar Mafa ta jihar Borno.
Gungun ‘yan ta’addan da aka hallaka Su 20 dake saman babura sun fito daga
Yammacin jihar ta mashiga Mafa akan hanyar su ta zuwa dajin Sambisa.
Zagazola ya ruwaito cewa dakarun sojin sun sami nasarar ne bayan samun wani rahoton sirri kan cewa ‘yan Ta’addan na kan hanyar Mafa
Sojojin bisa hadin Gwiwar dakarun sa kai na JTF suka yi musu kwanton bauna, nan take suka hallaka da dama cikin su.

Haka kuma sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Ta’addan a raye, yayin da wasu suka gudu cikin daji da raunin harbi a jikin su.
“kwanton baunar ya haifar da mummunar musayar wuta tsakanin mu, daga bisani sun fara shirin ranta a na kare, na muka bisu, saboda haka mun halaka da dama daga cikin su, wasu kuwa sun tsere da raunikan harbi a jikin su. A cewa majiyar.
Ya bayyana cewa 2 cikin dakarun CJTF sun ji rauni sakamakon musayar wuta, inda kuma suka sami nasarar kwato makamai da babura a hannun ‘yan Ta’addan

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp