Home General Sojojin Nijeriya sun Kama Wanda ya hallaka Ahmamad Gulak

Sojojin Nijeriya sun Kama Wanda ya hallaka Ahmamad Gulak

Dakarun rundunar sojojin Nijeriya sun kama mataimakain kwamandan mayakan kungiyar ‘yan awaren Biyafara IPOB Nwagwu Chiwendu, wanda ke hannun bisa kisan dan siyasar yankin Arewacin kasar Ahmed Gulak.
PRNigeria ta tattaro cewa Chiwendu shine mai horas da dakarun kungiyar sarrafa makamai, wanda ke matsayin na biyu cikin masu fada aji a tawagar, wanda kuma shine shugaban kungyar a jihar Imo.
Hamshakin dan Ta’addan ya bar aikin cikin rundunar soji Nijeriya, inda ya koma cikin kungiyar ta IPOB tun watan janairun 21.
“yayin aiki a cikin rundunar Operation hadin kai (OPHK) yana kuma cikin wanda suka sami horo, an kama shi jiya yayin bikin binne mahaifinsa a Mbaise. Ya kuma kai mu zuwa sansanin sun a Obowo da daddare.
“ya amsa cewa shine ya hallaka Gulak, ya kuma tabbatar da cewa sansanin ke da alhakin yin garkuwa da matafiya 2 akan hanyar Owerri zuwa Okigwe inda suka hallaka sifeton ‘yan sanda guda biyu dake musu rakiya.
haka kuma suke majiyar ta bayyanawa PRNigeria cewa, “sun eke da alhakin hallaka sojoji a wannan yanki tare ga kone motarsu kirar Hilux makon daya gabata. Haka kuma sun bada gudunmawa wajen kai hari ofishin hukumar zabe mai zaman kanta na INEC dake Owerri. Hanzu haka dai yana hannun jami’an ‘yan sanda.
By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp