Home General Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya tayi Martani ga kasashen Ketare

Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya tayi Martani ga kasashen Ketare

Bayan Birtaniya da Australia sun bukaci ‘yan kasarsu su guji zuwa Najeriya saboda dalilai na tsaro.

rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ce kasar na cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya har zuwa lokacin zabe, inda ta kara da cewa ba wannan ne karon farko da kasashen ketare ke fitar da sanarwar mai kama da wannan ba ga ‘yan kasarsu.

Tun da fari dai a cikin wani sakon shawarwari kan tafiye-tafiye, gwamnatin Australia ta bukaci janye duk wani shiri ko tunanin zuwa Najeriya ga ‘yan kasarta saboda ana shirin gudanar da manyan zabuka a kasar, kuma akwai fargabar da ake ta barkewar tashe-tashen hankula da ke da nasaba da zabe.

Cikin sakon, gwamantin ta Australia ta ce akwai zargin hare haren da ake kitsawa na kai hari kan ofisoshin hukumar zabe, don haka kasar ta shawarci ‘yan kasarta da su nisanta kansu da zuwa Najeriya.

Itama gwamnatin Birtaniya ta yi gargadin cewa za a iya samun barkewar zanga-zanga a lokacin zabe, don haka ne ta shawarci ‘yan kasarta da zaune a Najeriyar da ma wadanda ke shirin zuwa kasar da su guji zuwa Najeriya musamman a wannan lokaci da zabuka ke tafe a Najeriya.

Kazalika itama kungiyar Tarayyar Turai, ta yi gargadin cewa rashin tsaro na iya hana a gudanar da zabe a wasu sassan kasar ta Najeriya.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne dai kasashen Amurka da Birtaniya da Canada da Jamus da Bulgeriya suka fitar da sanarwar kan ta’addanci, inda suka gargadi ‘yan kasarsu a Najeriya da su guji manyan shagunan siyar da kayayyaki da wuraren ibada da otal-otal da suka ce ‘yan ta’adda za su iya kai wa hari.

Sai dai Gwamnatin Tarayyar kasar ta yi watsi da wannan gargadi, inda ta bayyana su a matsayin na karya, ta kuma ba ‘yan Najeriya tabbacin gudanar da harkokinsu bisa doka domin kasar na cikin kwanciyar hankali.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp