Home General Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya tayi Martani ga kasashen Ketare

Rundunar ‘Yan sandan Nijeriya tayi Martani ga kasashen Ketare

Bayan Birtaniya da Australia sun bukaci ‘yan kasarsu su guji zuwa Najeriya saboda dalilai na tsaro.

rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ce kasar na cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya har zuwa lokacin zabe, inda ta kara da cewa ba wannan ne karon farko da kasashen ketare ke fitar da sanarwar mai kama da wannan ba ga ‘yan kasarsu.

Tun da fari dai a cikin wani sakon shawarwari kan tafiye-tafiye, gwamnatin Australia ta bukaci janye duk wani shiri ko tunanin zuwa Najeriya ga ‘yan kasarta saboda ana shirin gudanar da manyan zabuka a kasar, kuma akwai fargabar da ake ta barkewar tashe-tashen hankula da ke da nasaba da zabe.

Cikin sakon, gwamantin ta Australia ta ce akwai zargin hare haren da ake kitsawa na kai hari kan ofisoshin hukumar zabe, don haka kasar ta shawarci ‘yan kasarta da su nisanta kansu da zuwa Najeriya.

Itama gwamnatin Birtaniya ta yi gargadin cewa za a iya samun barkewar zanga-zanga a lokacin zabe, don haka ne ta shawarci ‘yan kasarta da zaune a Najeriyar da ma wadanda ke shirin zuwa kasar da su guji zuwa Najeriya musamman a wannan lokaci da zabuka ke tafe a Najeriya.

Kazalika itama kungiyar Tarayyar Turai, ta yi gargadin cewa rashin tsaro na iya hana a gudanar da zabe a wasu sassan kasar ta Najeriya.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne dai kasashen Amurka da Birtaniya da Canada da Jamus da Bulgeriya suka fitar da sanarwar kan ta’addanci, inda suka gargadi ‘yan kasarsu a Najeriya da su guji manyan shagunan siyar da kayayyaki da wuraren ibada da otal-otal da suka ce ‘yan ta’adda za su iya kai wa hari.

Sai dai Gwamnatin Tarayyar kasar ta yi watsi da wannan gargadi, inda ta bayyana su a matsayin na karya, ta kuma ba ‘yan Najeriya tabbacin gudanar da harkokinsu bisa doka domin kasar na cikin kwanciyar hankali.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp