Home General Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban...

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo da ke kudu maso gabashin Najeriya sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar, bayan da suka sace shi a ranar Juma’ar da ta gabata.

‘Yan bindigar dai sun saki wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda suka ɗaure shugaban ƙaramar hukumar a hannaye, da kuma yadda suka halaka shi, bayan sun karɓi kuɗin fansa don su sako shi.

Wata majiya a rundunar ‘yan sandan Najeriya ta jihar Imo, ta tabbatar wa BBC labarin kisan gillar da ‘yan bindigar suka yi wa shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Ideato ta Arewa a jihar, mai suna Chris Ohizu, ƙasa da kwana biyu da sace shi.

Majiyar ‘yan sandan ta ce, rundunarsu tana ƙoƙarin ceto shugaban ƙaramar hukumar daga hannun ‘yan bindigan da suka sace shi, sai kwatsam a daren Lahadi aka yi aune da wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda aka durƙusar da shi kan gwiwoyinsa, a wani ƙungurmin daji, aka ɗaure masa hannaye a harɗe ta baya, daga bisani kuma aka sare masa kai.

Amma dai rundunar ‘yan sandan ta bayar da tabbacin tana ci gaba da gudanar da bincike, har sai ta zaƙulo waɗanda ake zargi da tafka wannan aika-aika.

A ɗaya daga cikin hotunan bidiyon da suka karaɗe shafukan sada zumunta, da ‘yan bindigan suka saki, an ji wata murya tana barazanar halaka shi kansa gwamnan jihar ta Imo, Hope Uzodimma nan ba da daɗewa ba.

Muryar ta kuma ce, su ba ‘yan kungiyar tsaro ta ESN ko kungiyar ‘yan a-waren Biafra ta IPOB ba ne. Su dai gungun wasu mutane ne da ke fafutukar tabbatar da kafuwar jamhuriyyar Biafra a yankin kudu maso gabashin Najeriya, inda suka lashi takobin ba za su bari a gudanar da babban zaben da ke tafe ba.

Ko da a ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka sace shugaban ƙaramar hukumar na riƙo, bayan sun harbe shi da bindiga a kafa, sannan suka banka wa gidansa wuta.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai gwamnatin jihar Imo ba ta ce uffa ba, game da aukuwar wannan lamari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp