Home General Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban...

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar

Wasu ‘yan bindiga a jihar Imo da ke kudu maso gabashin Najeriya sun sare kan wani shugaban ƙaramar hukumar Ideato ta arewa a jihar, bayan da suka sace shi a ranar Juma’ar da ta gabata.

‘Yan bindigar dai sun saki wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda suka ɗaure shugaban ƙaramar hukumar a hannaye, da kuma yadda suka halaka shi, bayan sun karɓi kuɗin fansa don su sako shi.

Wata majiya a rundunar ‘yan sandan Najeriya ta jihar Imo, ta tabbatar wa BBC labarin kisan gillar da ‘yan bindigar suka yi wa shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Ideato ta Arewa a jihar, mai suna Chris Ohizu, ƙasa da kwana biyu da sace shi.

Majiyar ‘yan sandan ta ce, rundunarsu tana ƙoƙarin ceto shugaban ƙaramar hukumar daga hannun ‘yan bindigan da suka sace shi, sai kwatsam a daren Lahadi aka yi aune da wasu hotunan bidiyo da ke nuna yadda aka durƙusar da shi kan gwiwoyinsa, a wani ƙungurmin daji, aka ɗaure masa hannaye a harɗe ta baya, daga bisani kuma aka sare masa kai.

Amma dai rundunar ‘yan sandan ta bayar da tabbacin tana ci gaba da gudanar da bincike, har sai ta zaƙulo waɗanda ake zargi da tafka wannan aika-aika.

A ɗaya daga cikin hotunan bidiyon da suka karaɗe shafukan sada zumunta, da ‘yan bindigan suka saki, an ji wata murya tana barazanar halaka shi kansa gwamnan jihar ta Imo, Hope Uzodimma nan ba da daɗewa ba.

Muryar ta kuma ce, su ba ‘yan kungiyar tsaro ta ESN ko kungiyar ‘yan a-waren Biafra ta IPOB ba ne. Su dai gungun wasu mutane ne da ke fafutukar tabbatar da kafuwar jamhuriyyar Biafra a yankin kudu maso gabashin Najeriya, inda suka lashi takobin ba za su bari a gudanar da babban zaben da ke tafe ba.

Ko da a ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka sace shugaban ƙaramar hukumar na riƙo, bayan sun harbe shi da bindiga a kafa, sannan suka banka wa gidansa wuta.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai gwamnatin jihar Imo ba ta ce uffa ba, game da aukuwar wannan lamari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp