Home General Bankunan kasuwanci sun dakatar da ayyukansu a Akure babban birnin jihar Ondo

Bankunan kasuwanci sun dakatar da ayyukansu a Akure babban birnin jihar Ondo

Bankunan kasuwanci sun dakatar da ayyukansu gaba daya a Akure babban birnin jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa dukkanin bankunan da wakilanta suka ziyarta a titin Oba Adesida da kuma Alagbaka a babban birnin jihar, kofofinsu na kulle.
Sai dai ta ce akwai tarin jama’a masu mu’amulla da bankin da suke tsaye curko-curko a wajen bankunan suna zaman jiran tsammani.
Daya daga cikin mutanen mai suna Jimoh ya bayyana cewa tun karfe 7:30 nsf (na safe) yake wurin.
Mutumin ya ce jami’an tsaron bankunan sun gaya masa cewa an rufe bankunan ne saboda tsoron kai musu hari.
kamar dai sauran sassan jihar ta Ondo can ma a garin Ikare-Akoko da ke yankin karamar hukumar Akoko Northeast ba a bude bankunan ba ga jama’a.
Jama’a na fama da wahalhalu sakamakon matakin Babban Bankin kasar na sauya fasalin wasu daga cikin manyan takardun kudin kasar na 1,000 da 500 da kuma 200.
Bankin ya sanya wa’adin daina karbar takardun a tsakanin jama’a zuwa ranar 10 ga watan nan na Fabrairu, to amma kuma a jiya laraba Kotun Kolin kasar ta yanke hukuncin shari’ar da gwamnonin jihohin Kogi da Kaduna da kuma Zamfara suka shigar gabanta kan hana wa’adin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp