Home General Dakarun Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a jihar Kaduna

Dakarun Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar ‘yan bindiga a jihar Kaduna

Dakarun sojojin Najeriya rukuni na huɗu da wasu dakaru na musamman na bataliya ta 167 sun kashe ‘yan bindiga tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.

Dakarun waɗanda suka shafe dogon lokaci suna bata kashi da ‘yan bindigar a yankin Ƙaramar Hukumar Chikun sun tashi wata maɓoyar ‘yan bindigar a lokacin rikicin.

Wannan na Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Samuel Aruwan ya fitar, inda yace “yayin wannan samame an ceto mutane 14, da suka hadar  da maza tara da mata biyar. An kai waɗanda aka ceto ɗin wani wuri mai aminci za a yi musu gwaje-gwaje kafin a haɗa su da iyalansu.”

A cewarsa a yayin wannan simamen, dakarun sun lalata sansanin ‘yan bindiyar da dama an kuma kwato wasu motoci biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp