Dakarun sojojin Najeriya rukuni na huɗu da wasu dakaru na musamman na bataliya ta 167 sun kashe ‘yan bindiga tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.
Dakarun waɗanda suka shafe dogon lokaci suna bata kashi da ‘yan bindigar a yankin Ƙaramar Hukumar Chikun sun tashi wata maɓoyar ‘yan bindigar a lokacin rikicin.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Wannan na Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Samuel Aruwan ya fitar, inda yace “yayin wannan samame an ceto mutane 14, da suka hadar da maza tara da mata biyar. An kai waɗanda aka ceto ɗin wani wuri mai aminci za a yi musu gwaje-gwaje kafin a haɗa su da iyalansu.”
A cewarsa a yayin wannan simamen, dakarun sun lalata sansanin ‘yan bindiyar da dama an kuma kwato wasu motoci biyu.
PRNigeria hausa










