Home Labarai Buhari ya bukaci ‘yan Nijeriya dasu karbi kudin zabe idan an basu

Buhari ya bukaci ‘yan Nijeriya dasu karbi kudin zabe idan an basu

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci jama’ar kasar da su karbi kudaden da ‘yan siyasa suke rabawa lokacin zabe, amma kuma su zabi abinda suke so.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan kada kuri’ar sa a zaben gwamnan jihar Katsina da na ‘yan majalisu, shugaban ya ce yana da yakinin jam’iyyarsa ta APC za ta sake samun nasara.

Shugaban ya ce ko kadan bai yi mamakin yadda sakamakon zaben shugaban kasar da aka yi ranar 25 ga watan Fabarairu ya kaya ba, wanda aka bayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya samu nasara.

Buhari ya ce Jam’iyyar APC ta gudanar da yakin neman zabe tukuru wajen bayyana manufofinta da shirin da take da shi ga jama’ar Najeriya.

Shugaban yace duk da yadda matsalar karancin kudi ta yiwa shirin sayen kuri’u dabaibayi, har yanzu wasu bata garin ‘yan siyasa na rabawa masu zabe kudade.

Buhari ya bai wa jama’a shawarar cewar su karbi kudinsu soke, kana su zabi abinda suke so.

Daga karshe shugaban ya jinjinawa ‘yan Najeriya akan amincewar da suka yi wa jam’iyyar su, yayin da su kuma suka saka musu wajen gudanar da ayyuka a bangaren ilimi da kula da lafiya da kuma gina kayan more rayuwa.

Shugaban ya kuma yabawa kafofin yada labarai saboda rawar da suka taka wajen wayar da kan jama’a domin zabin irin shugabannin da suke so da kuma tuhumarsu idan sun saba alkawarin da suka musu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp