Home Labarai Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya ta bayyana sakamakon zaɓen gwamnan jihar Kebbi a matsayin wanda bai kammala ba.

Babban jami’in tattara sakamakon zaɓen jihar Farfesa Yusuf Sa’idu na jami’ar Usman Danfodio da ke Sokoto ne ya bayyana haka a cibiyar karɓar sakamakon zaɓen da ke Birnin Kebbi.

Ya ce an samu yawan ƙuri’u da aka soke a rumfunan zaɓe da dama a faɗin ƙananan hukumomi 20, daga cikin 21 na jihar.

Fafatawar dai ta fi zafi ne tsakanin manyan jam’iyyun APC mai mulkin jihar da kuma jam’iyyar PDP mai hamayya.

Farfesa Sa’idu ya ce adadin katin zaɓen da aka karɓa a wuraren da aka soke zaɓen ya kai 91,829.

“Sakamakon da muka tattara yanzu ya nuna cewa jam’iyyar APC na da yawan ƙuri’u 388,258, yayin da PDP ke da ƙuri’a 342,980. Dan haka idan muka duba bambancin da ke tsakaninsu shi ne ƙuri’a 45,278,” in ji Farfesa Sa’idu.

Dan haka a cewarsa ba abin da ya kamata a yi sai komawa sashe 51 ƙaramin sashen biyu da na uku, na dokar zaɓe ta 2022.

Wanda ya tanadi cewa idan adadin ƙuri’un da aka soke ya zarta adadin tazarar ƙuri’un da ke tsakanin ‘yan takara to dole sai an sake zaɓe a wuraren da aka soke zaɓukan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp