Home Labarai Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya ta bayyana sakamakon zaɓen gwamnan jihar Kebbi a matsayin wanda bai kammala ba.

Babban jami’in tattara sakamakon zaɓen jihar Farfesa Yusuf Sa’idu na jami’ar Usman Danfodio da ke Sokoto ne ya bayyana haka a cibiyar karɓar sakamakon zaɓen da ke Birnin Kebbi.

Ya ce an samu yawan ƙuri’u da aka soke a rumfunan zaɓe da dama a faɗin ƙananan hukumomi 20, daga cikin 21 na jihar.

Fafatawar dai ta fi zafi ne tsakanin manyan jam’iyyun APC mai mulkin jihar da kuma jam’iyyar PDP mai hamayya.

Farfesa Sa’idu ya ce adadin katin zaɓen da aka karɓa a wuraren da aka soke zaɓen ya kai 91,829.

“Sakamakon da muka tattara yanzu ya nuna cewa jam’iyyar APC na da yawan ƙuri’u 388,258, yayin da PDP ke da ƙuri’a 342,980. Dan haka idan muka duba bambancin da ke tsakaninsu shi ne ƙuri’a 45,278,” in ji Farfesa Sa’idu.

Dan haka a cewarsa ba abin da ya kamata a yi sai komawa sashe 51 ƙaramin sashen biyu da na uku, na dokar zaɓe ta 2022.

Wanda ya tanadi cewa idan adadin ƙuri’un da aka soke ya zarta adadin tazarar ƙuri’un da ke tsakanin ‘yan takara to dole sai an sake zaɓe a wuraren da aka soke zaɓukan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp