Home Labarai EU ta bayar da miliyan 75 don magance cutar mashaƙo a Najeriya

EU ta bayar da miliyan 75 don magance cutar mashaƙo a Najeriya

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta bayar da tallafin dala 150,000, kwatankwacin naira miliyan 75 don yaƙi da yaɗuwar cutar mashaƙo a Najeriya.

Haka kuma gami taimaka wa al’umomin da suka kamu a jihohin Kano da Katsina da Legas da kuma Osun.

Tarayyar Turan ta ce ta ɗauki matakin ne sakamakon ƙaruwar yaɗuwar cutar a Najeriya tun farkon shekarar 2023.

Za a bayar da tallafin ne ga mutane sama da miliyan daya da rabi, inda za a fi bayar da fifiko kan mutanen da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar.

Waɗanda ke zaune a wurare masu wahalar zuwa, kamar yadda ƙungiyar ta EU ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.

Tallafin wani ɓangare ne taimakon da ƙungiyar ke haɗawa na tara asusu don magance aukuwar bala’o’i a ƙasashen duniya ta hanyar ƙungiyoyin Red Cross da Red Crescent.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp