Home Labarai Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada tsohon shugaban hukumar lura da jami’oin Nijeriya (Tetfund) Dr. Baffa bichi matsayin shugaban kwamitin karbar Mulki.

Wannan na kunshe ne cikin watan sanarwa da sakataren yada labaran zababben Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar wadda aka raba ga manema labarai a yammacin juma’a.

Inda Sanarwar ta bayyana cewa biyo bayan tabbatar masa da shaidar kasancewar s ana zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir yusuf ya nada kwamitin karbar Mulki daga hannun gwamanti mai shudewa.

Inda tsohon sakataren hukumar ta tetfund kuma wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP takarar sanata a santoriyar kano ta arewa a zaben 2023, Dr. Baffa Bichi matsayin shugaban kwamitin karbar mulkin Abdullahi Musa matsayi sakatare.

Aikin Kwamitin shine gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Haka kuma akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp