Home Labarai Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada tsohon shugaban hukumar lura da jami’oin Nijeriya (Tetfund) Dr. Baffa bichi matsayin shugaban kwamitin karbar Mulki.

Wannan na kunshe ne cikin watan sanarwa da sakataren yada labaran zababben Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar wadda aka raba ga manema labarai a yammacin juma’a.

Inda Sanarwar ta bayyana cewa biyo bayan tabbatar masa da shaidar kasancewar s ana zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir yusuf ya nada kwamitin karbar Mulki daga hannun gwamanti mai shudewa.

Inda tsohon sakataren hukumar ta tetfund kuma wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP takarar sanata a santoriyar kano ta arewa a zaben 2023, Dr. Baffa Bichi matsayin shugaban kwamitin karbar mulkin Abdullahi Musa matsayi sakatare.

Aikin Kwamitin shine gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Haka kuma akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp