Home Labarai Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada tsohon shugaban hukumar lura da jami’oin Nijeriya (Tetfund) Dr. Baffa bichi matsayin shugaban kwamitin karbar Mulki.

Wannan na kunshe ne cikin watan sanarwa da sakataren yada labaran zababben Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar wadda aka raba ga manema labarai a yammacin juma’a.

Inda Sanarwar ta bayyana cewa biyo bayan tabbatar masa da shaidar kasancewar s ana zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir yusuf ya nada kwamitin karbar Mulki daga hannun gwamanti mai shudewa.

Inda tsohon sakataren hukumar ta tetfund kuma wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP takarar sanata a santoriyar kano ta arewa a zaben 2023, Dr. Baffa Bichi matsayin shugaban kwamitin karbar mulkin Abdullahi Musa matsayi sakatare.

Aikin Kwamitin shine gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Haka kuma akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp