Home Labarai Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

President-Muhammadu-Buhari

Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

A karo na biyu, shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya ɗage kidayar 2023 da aka shirya gudanarwa a Najeriya.

Ya ɗauki wannan matakin ne bayan ganawa da shugaban NPC na ƙasa, Nasir Isa-Kwarra, da tawagarsa a fadar shugaban ƙasa.

A halin yanzun, Buhari ya bar wuƙa da nama hannun gwamnati mai zuwa karƙaashin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Abuja – Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya amince da sake ɗaga aiki kidayar mutane da gidaje a Najeriya na shekarar 2023.

Jaridar ta ce shugaban ƙasan ya ɗage aikin kidayar wanda aka tsara gudanarwa ranar 3 zuwa 7 ga watan Mayu, 2023, a yanzu ya bar wuƙa da nama hannun sabuwar gwamnati.

Buhari ya ɗauki wannan matakin ne a wurin ganawa da wasu mambobin majalisar zartaswa da shugaban hukumar kidaya ta ƙasa (NPC), Nasir Isa-Kwarra, da tawagarsa a Abuja ranar Jummu’a.

Wannan na ƙunshe a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai da safiyar Asabar mai ɗauke da sa hannun Ministan yaɗa labarai, Alhaji Lai Muhammed.

Sanarwan ta ce:

“Yayin da aka cimma matsayar sake ɗage aikin kidayar, taron ya kara jaddada muhimmancin kidayar yan Najeriya da gidaje, shekaru 17 bayan gudanar da kidaya a Najeriya.”

“Hakan ne kaɗai zai sa a tattara bayanai waɗanda zasu taimaka wajen cika burin kawo ci gaba a ƙasar nan kuma ya daidaita walwaha a rayuwar mazauna Najeriya.”

A wurin taron, an ji shugaba Muhammadu Buhari na cewa an cimma nasarori masu yawa a shirye-shiryen gudanar da kidaya, wacce aka ɗaga yanzu.

Ya kuma yaba wa hukumar kidaya ta ƙasa NPC bisa yadda ta ɗauki tsaruka da hanyoyin gudanar da sahihiyar kidaya wacce za’a dogara da ita a gwamnatance.

Jiga-jigan da suka halarci zaman Manyan kusoshin gwamnati da suka je wurin taron sun kunshi, Antoni Janar kuma ministan shari’a, Abubakar Malami, ministan yaɗa labarai, Lai Muhammed, Ministar kudi, kasafi da tsare-tsaren ƙasa, Zainab Ahmed.

Sauran su ne, ƙaramin ministan kasafi da tsare-tsaren ƙasa, Mista Clem Agba, da kuma Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp