Home DUNIYA Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Tsohon Firaministan Sudan Abdallah Hamdok ya yi gargaɗin cewa rashin tsaron da ƙasar ke fuskanta zai iya zarta na Siriya da Libya.

Mista Hamdok na wannan maganar ne yayin da ake ci gaba da samun rahotonnin kai farmaki da jiragen sama a kan wuraren da ke hannun dakarun RSF a birnin Khartoum.

Duk ɓangarori biyun da ke yaƙi da juna na zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta. Dubban mutane ne suka fice daga gidajensu sakamakon yaƙin.

Tsohon Firamistan ya bayyana yaƙin da rashin hankali tare da cewa yaƙi ne da babu wanda zai yi nasara a cikinsa, sai dai hasarar rayuka masu yawa da zai haifar.

Ya ce akwai buƙatar ƙasashen duniya su yi aiki tare domin zaunar da shugabanin rundunonin da ke yaƙi da juna a ƙasar da jagoran dakarun RSF a teburiun sulhu domin kawo ƙarshen yaƙin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp