Home DUNIYA Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Tsohon Firaministan Sudan Abdallah Hamdok ya yi gargaɗin cewa rashin tsaron da ƙasar ke fuskanta zai iya zarta na Siriya da Libya.

Mista Hamdok na wannan maganar ne yayin da ake ci gaba da samun rahotonnin kai farmaki da jiragen sama a kan wuraren da ke hannun dakarun RSF a birnin Khartoum.

Duk ɓangarori biyun da ke yaƙi da juna na zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta. Dubban mutane ne suka fice daga gidajensu sakamakon yaƙin.

Tsohon Firamistan ya bayyana yaƙin da rashin hankali tare da cewa yaƙi ne da babu wanda zai yi nasara a cikinsa, sai dai hasarar rayuka masu yawa da zai haifar.

Ya ce akwai buƙatar ƙasashen duniya su yi aiki tare domin zaunar da shugabanin rundunonin da ke yaƙi da juna a ƙasar da jagoran dakarun RSF a teburiun sulhu domin kawo ƙarshen yaƙin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp