Home DUNIYA Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Rikicin Sudan ka iya zamar wa duniya ƙarfe-ƙafa – Abdallah Hamdok

Tsohon Firaministan Sudan Abdallah Hamdok ya yi gargaɗin cewa rashin tsaron da ƙasar ke fuskanta zai iya zarta na Siriya da Libya.

Mista Hamdok na wannan maganar ne yayin da ake ci gaba da samun rahotonnin kai farmaki da jiragen sama a kan wuraren da ke hannun dakarun RSF a birnin Khartoum.

Duk ɓangarori biyun da ke yaƙi da juna na zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta. Dubban mutane ne suka fice daga gidajensu sakamakon yaƙin.

Tsohon Firamistan ya bayyana yaƙin da rashin hankali tare da cewa yaƙi ne da babu wanda zai yi nasara a cikinsa, sai dai hasarar rayuka masu yawa da zai haifar.

Ya ce akwai buƙatar ƙasashen duniya su yi aiki tare domin zaunar da shugabanin rundunonin da ke yaƙi da juna a ƙasar da jagoran dakarun RSF a teburiun sulhu domin kawo ƙarshen yaƙin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp