Home Labarai Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin Bauchi ta ce za ta dauki matasa akalla dubu 20,000 aiki domin yakar matsalar tsaro da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, karkashin wata rundunar tsaro da za ta kirkiro ta musamman a jihar.

An ruwaito cewa rundunar tsaron za ta kasance ne kamar wadda jihohin kudu maso yammacin kasar suka kirkiro wadda ake kira Amotekum.

Gwamnan jihar Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ne ya bayyana matakin jim kadan da sake rantsar da shi a wa’adi na biyu a matsayin gwamnan a jiya Litinin.

Mai sharia Rabi Talatu ce ta rantsar da shi tare da mataimakinsa Mohammed Auwal Jatau a lokacin.

Gwamnan ya ce rundunar wadda za ta taimaka gaya ga tsarin tsaron da tuni ake da shi a kananan hukumomin jihar za ta kunshi matasa 20,000 da za a fara dauka a kashin farko.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp