Home Labarai Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin Bauchi ta ce za ta dauki matasa akalla dubu 20,000 aiki domin yakar matsalar tsaro da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, karkashin wata rundunar tsaro da za ta kirkiro ta musamman a jihar.

An ruwaito cewa rundunar tsaron za ta kasance ne kamar wadda jihohin kudu maso yammacin kasar suka kirkiro wadda ake kira Amotekum.

Gwamnan jihar Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ne ya bayyana matakin jim kadan da sake rantsar da shi a wa’adi na biyu a matsayin gwamnan a jiya Litinin.

Mai sharia Rabi Talatu ce ta rantsar da shi tare da mataimakinsa Mohammed Auwal Jatau a lokacin.

Gwamnan ya ce rundunar wadda za ta taimaka gaya ga tsarin tsaron da tuni ake da shi a kananan hukumomin jihar za ta kunshi matasa 20,000 da za a fara dauka a kashin farko.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp