Home Labarai Ba za mu bar tsibirin Tafkin Chadi ko daya a hannun ‘yan...

Ba za mu bar tsibirin Tafkin Chadi ko daya a hannun ‘yan ta’adda ba – MNJTF

Kwamandan rundunar sojin hadin gwiwar da ke yaki da ‘yan ta’adda a yankin tafkin Chadi ta MNJTF, Manjo Janar Gold Chinuisi, ya bayyana aniyarsa ta ganin sun murkushe duk mayakan Boko Haram da na ISWAP da ke zama a tsibiran da suke kewaye da tafkin baki daya.

Janar Chinuisi ya bayyana haka ne, lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a Balangoua da ke kasar Kamaru, da kuma Bagasola da Bibi da ke cikin kasar Chadi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Babban jami’in hulda da jama’a na rundunar ta MNJTF, laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, ya ce Kwamandan ya bayyana karara cewar, ya  kai ziyarar ce domin tantance karfin rundunonin da ke bakin aiki daga da kuma karfafa musu guiwa wajen ganin sun cigaba da jajircewa a yakin da suke gwabzawa, yayin da ya yi musu alkawarin taimakon da suke bukata domin samun nasara.

Kanal Abdullahi ya ce kafa rundunar MNJTF ta taka rawa gaya wajen dakile kaifin mayakan Boko Haram wajen shirya kai hari a tsibiran da ke Tafkin Chadi da ake kira Tumbus, yayin da janar Chibuisi ya bukaci sojojin da suk dada kara kaimi wajen dorawa akan nasarorin da suka samu, domin kawar da mayakan daga tsibirin.

Ziyarar aikin ta Kamaru da Chadi na zuwa ne kwana guda bayan kammala irinta da Kwamandan ya kai Malam Fatori da ke Najeriya da kuma Diffa da Bosso a Jamhuriyar Nijar, a kokarin da sojojin ke yi na kawar da ayyukan ta’adddanci a yankin Tafkin Chadi baki daya domin mayar da zaman lafiya..

Kanal Abdullahi ya ce Janar Chibuisi ya sha alwashin bai wa dakarun goyon bayan da suke bukata domin samun nasarar yakin baki daya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp