Home Labarai Ba za mu bar tsibirin Tafkin Chadi ko daya a hannun ‘yan...

Ba za mu bar tsibirin Tafkin Chadi ko daya a hannun ‘yan ta’adda ba – MNJTF

Kwamandan rundunar sojin hadin gwiwar da ke yaki da ‘yan ta’adda a yankin tafkin Chadi ta MNJTF, Manjo Janar Gold Chinuisi, ya bayyana aniyarsa ta ganin sun murkushe duk mayakan Boko Haram da na ISWAP da ke zama a tsibiran da suke kewaye da tafkin baki daya.

Janar Chinuisi ya bayyana haka ne, lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a Balangoua da ke kasar Kamaru, da kuma Bagasola da Bibi da ke cikin kasar Chadi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Babban jami’in hulda da jama’a na rundunar ta MNJTF, laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, ya ce Kwamandan ya bayyana karara cewar, ya  kai ziyarar ce domin tantance karfin rundunonin da ke bakin aiki daga da kuma karfafa musu guiwa wajen ganin sun cigaba da jajircewa a yakin da suke gwabzawa, yayin da ya yi musu alkawarin taimakon da suke bukata domin samun nasara.

Kanal Abdullahi ya ce kafa rundunar MNJTF ta taka rawa gaya wajen dakile kaifin mayakan Boko Haram wajen shirya kai hari a tsibiran da ke Tafkin Chadi da ake kira Tumbus, yayin da janar Chibuisi ya bukaci sojojin da suk dada kara kaimi wajen dorawa akan nasarorin da suka samu, domin kawar da mayakan daga tsibirin.

Ziyarar aikin ta Kamaru da Chadi na zuwa ne kwana guda bayan kammala irinta da Kwamandan ya kai Malam Fatori da ke Najeriya da kuma Diffa da Bosso a Jamhuriyar Nijar, a kokarin da sojojin ke yi na kawar da ayyukan ta’adddanci a yankin Tafkin Chadi baki daya domin mayar da zaman lafiya..

Kanal Abdullahi ya ce Janar Chibuisi ya sha alwashin bai wa dakarun goyon bayan da suke bukata domin samun nasarar yakin baki daya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp