Home DUNIYA Matakin Soji zai zama na karshe kan sojojin Nijar – Manyan Hafsoshin...

Matakin Soji zai zama na karshe kan sojojin Nijar – Manyan Hafsoshin ECOWAS

Manyan hafsoshin tsaron ƙungiyar Ecowas za su samar da mafita idan dukkan hanyoyin da aka bi a siyasance ba su yi tasiri ba bayan juyin mulki a Nijar.

Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya, Birgediya JanarTukur Gusau ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron da suka gudanar, in da yace matakin soji zai zamo na karshe.

“Matakin soji zai zama na ƙarshe da za a ɗaukar kan dakarun sojojin da suka yi Juyin Mulki a kasar, ”

Manyan hafsoshin tsaron ƙungiyar ta raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma na tattaunawa a Abuja daga yau Laraba zuwa Juma’a domin tattaunawa kan hanyoyin da za a bi wajen shawo kan sojojin da suka yi juyin mulkin, inda aka hamɓarrar da gwamnatin Shugaba Mohamed Bazoum a makon da ya gabata.

Manyan hafsoshin tsaron Ghana, da Najeriya, da Benin, da Togo, da Saliyo, da Laberiya, da Gambiya, da Cote D’Ivoire, da Cape Verde ne ke halartar taron.

Sai dai takwarorinsu na Mali, da Nijar, da Guinea Bissau, da Burkina Faso, da Guinea ba su halarta ba sakamakon dakatar da su da Ecowas ta yi daga ƙungiyar saboda juyin mulkin da suka jagoranta a ƙasashensu.

Manyan hafsoshin tsaron za su gabatar da matakin da suka cimma ga shugaban ƙungiyar Bola Tinubu a ranar Juma’a.

Daga nan ne shugaban ƙungiyar zai yanke shawara kan mataki na gaba da za a ɗauka kan sojojin ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya ayyana kan sa a matsayin shugaban Nijar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp