Home Labarai WSCIJ ta yaba da kwazon jaridun PRNigeria da Economic confidential

WSCIJ ta yaba da kwazon jaridun PRNigeria da Economic confidential

Cibiyar binciken kwakwafi ta Wole Soyika ta yabawa da kwazon jaridun PRNigeria da Economic confidential.

Cibiyar binciken kwakwafi ta Wole Soyinka, WSCIJ ta bayyana gamsuwarta bisa kokarin Jaridun PRNigeria da Economic Confidential suka nuna a wani hadin gwiwa da tayi da su domin cigaba.

Dukkan jaridun na  PRNigeria da Economic Confidential, wani yanki ne dake karkashin inuwar kamfanin Image Merchants Promotion (IMPR), na cikin zababben kafafen yada labarai 26 da cibiyar ta WSCIJ zaba bisa tallafin  gidauniyar MacArthur.

Babbar daraktan cibiyar Mrs. Motunrayo Alaka, ta bayyana hakan yayin da  jagorancin tawagar cibiyar zuwa babban ofishin Jaridar dake Abuja, domin bayyana kokarin jaridun.

Ta  yabawa jaridun guda biyu dake karkashin kamfanin na IMPR bisa yadda suke wallafa sahihan labarai masu muhimmancin gaske.

Da yake nasa jawabin babban Editan Jaridun Mal. Yushau Shuaib ya bayyana cewa jaridun sun wallafa Labarin binciken kwakwafi, rahotanni na musamman da ya ja hankalin Mahukunta suka dauki mataki kan wasu lamurran da suka shafi al’ummomin  Niger, Zamfara, Kebbi da kuma birnin tarayya Abuja.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp