Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 36 tare da kwato mutane 140...

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 36 tare da kwato mutane 140 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace cikin makwanni 2 dakarunta sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda 137 tare da hallaka’ 36 a fadin kasar.

Haka Kuma cikin makwanni biyun ta sami nasarar ceto mutane 140 daga hannun ‘yan bindigar.

Daraktan sashen yada labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar mako – mako da ya fita a birnin tarayya Abuja.

Yace a yayin atisayen dakarun sun kama’ yan bindiga 3, masu garkuwa da mutane 2, sai wadanda ake hadin baki da su mutum 6 sai kuma barin danyen mai su 15 inda suka samu kudi har naira 3,177,650.00.

Janar Buba yace maza da mata a a cikin dakarun sojin Nijeriya sun shirya yaki da dukkan aikin bata gari.

“a shirye muke mu yake su, ya zama waji mu kakkabe su daga cikin mu.”

Yace a cikin makwanni dakarun sun sami nasarar kwato makamai 37 da alburusai 370, bindiga kirar ak47 guda 16, bindiga kirar pump action guda 6, kirar dane guda sai kuma karamar bindiga kirar gida 2 da dai sauran muggan makamai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp