Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 36 tare da kwato mutane 140...

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 36 tare da kwato mutane 140 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace cikin makwanni 2 dakarunta sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda 137 tare da hallaka’ 36 a fadin kasar.

Haka Kuma cikin makwanni biyun ta sami nasarar ceto mutane 140 daga hannun ‘yan bindigar.

Daraktan sashen yada labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar mako – mako da ya fita a birnin tarayya Abuja.

Yace a yayin atisayen dakarun sun kama’ yan bindiga 3, masu garkuwa da mutane 2, sai wadanda ake hadin baki da su mutum 6 sai kuma barin danyen mai su 15 inda suka samu kudi har naira 3,177,650.00.

Janar Buba yace maza da mata a a cikin dakarun sojin Nijeriya sun shirya yaki da dukkan aikin bata gari.

“a shirye muke mu yake su, ya zama waji mu kakkabe su daga cikin mu.”

Yace a cikin makwanni dakarun sun sami nasarar kwato makamai 37 da alburusai 370, bindiga kirar ak47 guda 16, bindiga kirar pump action guda 6, kirar dane guda sai kuma karamar bindiga kirar gida 2 da dai sauran muggan makamai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp