Home General Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta Asibitocin PHCs a jihar

Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta Asibitocin PHCs a jihar

Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko na (PHCs) a wani yunkuri na inganta harkokin lafiya  a jihar da kuma inganta manyan asibitoci domin inganta bangaren lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Habu Dahiru, ne ya bayyana hakan yayi  da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya wato NAN a wata ziyarar gani da ido da kamfanin ya kai ranar alhamis.

Haka kuma kwamishinan ya kara da cewa a wani shirin hadin gwiwa da gwamnatin jihar tayi da Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya, (UNICEF) wanda aka gyara asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko (PHC) guda 114 domin kara karfafawa gami da inganta matakin lafiyar.

A cewar Mr. Dahiru, gwamnatin jihar na gudanar da aikin jinya don gano tare da tura ta tura yara masu fama da lalurar tamowa da mata masu juna biyu da ba basa samun damar zuwa asibiti domin haihuwa ta hanyar daukar matakai da dama.

Yace sama da ma’aikatan lafiya 600 da suka hadar da Ungozoma, ma’aikatan lafiyar al’umma, CHEW, aka tura zuwa asibitocin na matakin farko PHC a fadin kananan hukumomin jihar 11.

Daga bisani ya tabbatar da cewa daukar wannan mataki ya taimaka wajen rage yawan mutuwar nata masu juna biyu a fadin jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp