Home Labarai Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kwamitin Kwamishinonin Lafiya na Arewa maso Gabashin Najeriya ya nemi tallafi daga Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, (NEDC) da ta tallafa wajen rage yawan mace-macen mata da jarirai a shiyoyin ƙasar.

Ya ce kashi 30 cikin 100 na mace-macen mata masu juna biyu da jariran da aka haifa a duniya suna faruwa ne a Najeriya.

Shugaban kwamitin, Farfesa Baba Mallam Gana ya bayyana hakan ne a wata ganawa da shugabannin hukumar NEDC kan hanyoyin inganta harkar lafiya a yankin.

Ya ce matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai da sauran matsalolin da suka shafi mata masu juna biyu da ke dagula harkar lafiya a yankin arewa maso gabas na da matukar muhimmanci a magance su.

“Bangaren kiwon lafiya a yankin Arewa maso Gabas na cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu, musamman idan aka yi la’akari da yanayin mata da jarirai da yaran da ake haifa.

“Hukumar NEDC ta yi ayyuka da yawa a fannin kiwon lafiya, amma a gaskiya, a yanzu mun fi buƙatar hukumar.

“Mu na da masaniya kan ayyukan hukumar, kamar inganta asibitin ido zuwa matsayin kasashen duniya. Yanzu, za mu yi aiki tare da Hukumar NEDC don inganta harkokin kiwon lafiyar al’ummar Arewa maso Gabas,” in ji Gana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp