Home Labarai Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kwamitin Kwamishinonin Lafiya na Arewa maso Gabashin Najeriya ya nemi tallafi daga Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, (NEDC) da ta tallafa wajen rage yawan mace-macen mata da jarirai a shiyoyin ƙasar.

Ya ce kashi 30 cikin 100 na mace-macen mata masu juna biyu da jariran da aka haifa a duniya suna faruwa ne a Najeriya.

Shugaban kwamitin, Farfesa Baba Mallam Gana ya bayyana hakan ne a wata ganawa da shugabannin hukumar NEDC kan hanyoyin inganta harkar lafiya a yankin.

Ya ce matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai da sauran matsalolin da suka shafi mata masu juna biyu da ke dagula harkar lafiya a yankin arewa maso gabas na da matukar muhimmanci a magance su.

“Bangaren kiwon lafiya a yankin Arewa maso Gabas na cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu, musamman idan aka yi la’akari da yanayin mata da jarirai da yaran da ake haifa.

“Hukumar NEDC ta yi ayyuka da yawa a fannin kiwon lafiya, amma a gaskiya, a yanzu mun fi buƙatar hukumar.

“Mu na da masaniya kan ayyukan hukumar, kamar inganta asibitin ido zuwa matsayin kasashen duniya. Yanzu, za mu yi aiki tare da Hukumar NEDC don inganta harkokin kiwon lafiyar al’ummar Arewa maso Gabas,” in ji Gana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp