Home Labarai Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kaso 30 na mace-macen Jarirai a Duniya na faruwa ne a Najeriya’

Kwamitin Kwamishinonin Lafiya na Arewa maso Gabashin Najeriya ya nemi tallafi daga Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, (NEDC) da ta tallafa wajen rage yawan mace-macen mata da jarirai a shiyoyin ƙasar.

Ya ce kashi 30 cikin 100 na mace-macen mata masu juna biyu da jariran da aka haifa a duniya suna faruwa ne a Najeriya.

Shugaban kwamitin, Farfesa Baba Mallam Gana ya bayyana hakan ne a wata ganawa da shugabannin hukumar NEDC kan hanyoyin inganta harkar lafiya a yankin.

Ya ce matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai da sauran matsalolin da suka shafi mata masu juna biyu da ke dagula harkar lafiya a yankin arewa maso gabas na da matukar muhimmanci a magance su.

“Bangaren kiwon lafiya a yankin Arewa maso Gabas na cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu, musamman idan aka yi la’akari da yanayin mata da jarirai da yaran da ake haifa.

“Hukumar NEDC ta yi ayyuka da yawa a fannin kiwon lafiya, amma a gaskiya, a yanzu mun fi buƙatar hukumar.

“Mu na da masaniya kan ayyukan hukumar, kamar inganta asibitin ido zuwa matsayin kasashen duniya. Yanzu, za mu yi aiki tare da Hukumar NEDC don inganta harkokin kiwon lafiyar al’ummar Arewa maso Gabas,” in ji Gana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp