Home Labarai Yadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja

Yadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja

Gwamman ma’aikatan jinya da ungozama ne suka hau titunan birnin Abuja domin nuna kin amincewarsu ga wasu sabbin dokoki da hukumar kula da ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa ta shimfida musu.

Sabbin dokokin dai sun hadar da kwashe shekaru biyu wadanda suka karanci aikin jinya a jami’a suna aiki a Najeriya kafin hukumar ta tantance su a matsayin kwararrun ma’aikatan jinya. Hukumar ta kuma kara kudin tantancewar daga dubu 29 zuwa dubu 300.

To sai dai kungiyar ma’aikatan jinyar ta ce kudin ya yi yawa kasancewar a cikinsu akwai wadanda suke daukar albashin da bai wuce naira dubu 50 ba a wata.

Ma’aikatan lafiya dai a Najeriya na yawan ficewa daga kasar da zarar sun samu lasisin aiki zuwa wasu kasashen ketare.

Sau da dama dai ma’aikatan lafiya a Najeriya na kokawa kan rashin isasshiyar kulawa da suke samu ciki har da albashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp