Home Labarai Har yanzu shigowa da shinkafa Nijeriya daga waje laifi ne – Tinubu

Har yanzu shigowa da shinkafa Nijeriya daga waje laifi ne – Tinubu

Fadar shugaban Nijeriya ta ce umarnin bude iyakokin kasar da jamhuriyar Nijar da Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayar, ba wai yana nufin bada damar shigo da kayan masarufi da sauran kayayyakin da tsohuwar gwamnatin Buhari ta hana shigo da su kasar ba ne.

”Wannan umarnin yana magana ne kawai akan abubunwan da suka faru ko matakan da ECOWAS ta dauka na sanyawa ƙasar Nijar takunkumi sakamakon Juyin mulki da sojojin kasar suka yi, don haka umarnin shugaban kasar yana magana ne kawai a koma Inda ake a bara “.

Babban Mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labarai Abdulaziz Abdulaziz ne ya bayyana hakan, yayin da yake Karin bayani ga manema labarai ta wayar tarho dangane da umarnin da shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar na bude iyakokin Nigeria da jamhoriyar Nijar.

Yace umarnin ba wai yana nufin a cigaba da shigo da kayan masarufi da sauransu ba ne, “dokokin mu na cikin gida na hukumar kwastam suna nan kuma jami’an hukumar zasu cigaba sa sanya idanu akan duk kayan da za’a Shigo da su Nijeriya.

”Kamar yadda aka sani a dokokin hukumar Kwastam akwai kayan da aka aminta da su akwai kuma wadanda ba’a aminta a shigo da su ba, don haka dokar da aka sa a baya tana nan tana aiki musamman akan shinkafa da wasu sauran abubuwan amfani na yau da kullum har yanzu dokar tana nan tana aiki aka su”.

Idan za’a iya tunawa tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammad Buhari shi ne ya rufe iyakokin kasar inda aka hana shigo da Shinkafa, kayan masarufi da sauransu da nufin inganta wadanda ake samar wa a cikin gida Nigeria.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp